Rashin Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Sanya Labule da CDS, Sarakunan Gargajiya

Rashin Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Sanya Labule da CDS, Sarakunan Gargajiya

  • Gwamnonin jihohin Arewa sun gudanar da taro kan matsalolin da suka daɗe suna ci wa yankin tuwo a ƙwarya
  • Taron an yi shi ne tare da babban hafsan sojoji (CDS) Christopher Musa da sauran manyan sarakunan gargajiya da masu ruwa da tsaki
  • CDS Christopher Musa ya yi bayani kan irin ƙoƙarin da sojoji ke yi domin kawo ƙarshen matsalar ƴan bindiga da ƴan ta'adda a yankin

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Kaduna - Gwamnonin jihohin Arewa 19 sun gana da sarakunan gargajiya na yankin a jihar Kaduna.

Gwamnonin na Arewa sun yi taron ne inda suka tattauna muhimman batutuwan da suka shafi yankin.

Gwamnonin Arewa sun yi taro a Kaduna
Gwamnonin Arewa sun gana da masu ruwa da tsaki a Kaduna Hoto: @ImranMuhdz
Asali: Twitter

Tashar Channels tv ta rahoto cewa an gudanar da taron ne a ranar Litinin a gidan gwamnatin jihar Kaduna.

Kara karanta wannan

Miyagun ƴan bindiga sun yi garkuwa da wani babban malami a Najeriya

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnonin Arewa sun yi taro

Taron dai na ɗaya daga cikin ƙoƙarin gwamnonin ke yi na yin tattaunawa da masu ruwa da tsaki domin magance matsalolin da suka addabi yankin musamman tabarbarewar tsaro, fatara da yaran da ba su zuwa makaranta.

Taron wanda Gwamna Uba Sani ya zama mai masauki baƙi, ya kasance ƙarƙashin jagorancin shugaban ƙungiyar gwamnonin Arewa kuma gwamnan jihar Gombe Inuwa Yahaya.

Taron ya samu halartar gwamnonin Kaduna, Gombe, Zamfara, Nasarawa, Borno, Borno, Bauchi, Kwara da Adamawa. Haka kuma akwai mataimakan gwamnonin wasu jihohin Arewa.

Babban hafsan sojoji (CDS), Janar Christopher Musa shi ma ya halarci taron ya kuma bayyanawa gwamnonin ƙoƙarin da sojoji ke yi domin magance matsalar ƴan bindiga da sauran matsalolin tsaro da suka addabi yankin Arewa.

Sarakunan gargajiya da suka halarci taron sun haɗa da Sarkin Musulmi Abubakar Saad, Shehun Borno, Umar El-Kanemi, Sarkin Zazzau, Nuhu Bamali, Ohinoyi na Ebira, Etsu Nupe, Yahaya Abubakar, Sarkin Kazaure da Sarkin Bauchi.

Kara karanta wannan

Matawalle: Dalilin Tinubu na barin minista da ake zargi da "daukar nauyin 'yan bindiga"

Ƴan Arewa sun caccaki Tinubu

A wani labarin kuma, kun ji cewa shugaban kasa Bola Tinubu ya fara shan suka kan umarnin da ya ba ministocin na rage tawaga da jami'an tsaro.

Kungiyar League of Northern Democrats ta ce babu alamar cewa shugaban kasar da gaske yake kan umarnin da ya bayar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng