Wata Jihar Arewa Ta Sake Ficewa daga Shari'ar Neman Rusa Hukumar EFCC

Wata Jihar Arewa Ta Sake Ficewa daga Shari'ar Neman Rusa Hukumar EFCC

  • Gwamnatin juhar Jigawa ta sanar da ficewarta daga ƙarar da ke neman a soke hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arziƙin ƙasa zagon ƙasa (EFCC)
  • Antoni Janar kuma kwamishinan shari'a na jihar ya sanar da janyewar a ranar Asabar, 26 ga watan Oktoban 2024
  • Bello Abdulkadir-Fanini ya bayyana cewa jihar ta shigar da buƙatar neman janyewa daga ƙarar ne a ranar 24 ga watan Oktoban 2024 a Kotun Ƙoli

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Jigawa - Gwamnatin Jigawa ta bayyana matsayarta kan ƙarar da wasu gwamnoni suka shigar ta neman a rusa hukumar EFCC.

Gwamnatin ta ce ta janye daga ƙarar wacce ke ƙalubalantar dokokin da suka kafa hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arziƙin ƙasa zagon ƙasa (EFCC) a Kotun Ƙoli.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun kai hari kusa da babbar jami'a, an rasa rayuka

Jigawa ta hanye daga karar EFCC
Jigawa ta janye daga shari'ar neman rusa EFCC Hoto: @uanamadi, @OfficialEFCC
Asali: Twitter

Antoni Janar kuma kwamishinan shari’a na jihar, Bello Abdulkadir-Fanini ne ya sanar da janyewar a taron manema labarai a birnin Dutse ranar Asabar, cewar rahoton jaridar Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jigawa ta janye daga ƙarar EFCC

Bello Abdulkadir-Fanini ya ce an shigar da buƙatar janyewar jihar daga ƙarar ne a ranar 24 ga watan Oktoban 2024, rahoton jaridar The Nation ya tabbatar.

"Bari a daidai nan gaɓar na sanar da cewa gwamnatin jihar Jigawa ta janye daga shari'ar Antoni Janar na Kogi VS Antoni Janar na tarayya mai lamba SC/CV/178/2023), wacce ke a Kotun Ƙoli."
"Buƙatar janyewar wacce na sanyawa hannu an shigar da ita a Abuja a ranar, 24 ga watan Oktoban 2024."

- Bello Abdulkadir-Fanini

Sai dai kwamishinan shari'ar bai bayyana dalilin da ya sa jihar ta janye daga ƙarar ba.

Karanta wasu labaran kan EFCC

Kara karanta wannan

Jam'iyyar PDP ta sake dage taron NEC, ta bayyana dalili

Gwamnan Zamfara baya tsoron EFCC

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa ba ya tsoron hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arziƙin ƙasa zagon ƙasa (EFCC).

A cewar Gwamna Dauda, ya kamata mutanen da aka zaɓa a kan muƙaman shugabanci su kasance masu riƙon amana da gaskiya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng