Ambaliyar Ruwa: An Shiga Jimami bayan Mutane da Dama Sun Rasa Matsugunansu

Ambaliyar Ruwa: An Shiga Jimami bayan Mutane da Dama Sun Rasa Matsugunansu

  • Mutane masu yawa sun rasa matsugunansu bayan an samu ambaliyar ruwa a ƙaramar hukumar Obio/Akpor ta jihar Rivers
  • Jama'a sun koka da cewa ambaliyar ruwan ta tilasta musu barin gidajensu bayan macizai sun mamaye inda suke rayuwa
  • Mutanen da ke yankin Rumaholu-Nkpolu sun yi kira ga gwamnatin jihar kan ta gina musu magudanun ruwa domin gaba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Rivers - Sama da iyalai 200 ne a yankin Rumaholu-Nkpolu da ke ƙaramar hukumar Obio/Akpor a jihar Rivers suka rasa matsugunansu sakamakon ambaliyar ruwa.

Hakan dai ya faru ne yayin da mazauna garin suka ce macizai sun mamaye gidajensu sakamakon mummunar ambaliyar ruwan.

Ambaliyar ruwa ta auku a Rivers
An samu ambaliyar ruwa a Rivers Hoto: Legit.ng
Asali: Original

Ambaliya ta yi ɓarna a Rivers

Kara karanta wannan

Ana kukan lantarki, ruwa ya karya gadar da ta haɗa ƙauyuka sama da 50

Mazauna yankin sun shaidawa jaridar The Punch cewa sun fara fuskantar irin wannan ambaliya ne a shekarar 2017 bayan da wasu mutane suka gina gidaje a magudanun ruwa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ɗaya daga cikin mutanen da lamarin ya shafa mai suna Thomas, ya ce a duk lokacin da ambaliyar ta afku, za su shafe kimanin watanni bakwai ba sa cikin gidajensu duk shekara suna jiran ruwan ya janye.

Ya bayyana cewa a wannan shekarar sun gudu daga gidajensu bayan sun ga macizai na fitowa daga cikin ruwan.

"Idan yanzu na kai ku cikin kowane gida da aka fita aka bari, za a samu macizai kusan guda shida."
"A cikin dare, idan babu fitila musamman yayin da ake saukowa daga kan matakala, za a ga macizai. Wani lokaci, kusan muna taka macizai, shi ya sa yawancin mu suka gudu."

Kara karanta wannan

Gwamna ya yi barazanar sauke sarakuna saboda rashin tsaro

- Thomas

Sun miƙa kokensu ga gwamnati

Wata mata da ta nemi a sakaya sunanta ta yi kira ga gwamnatin jihar Rivers da ta kawo musu ɗauki ta hanyar gina magudanun ruwa a yankin.

"Muna kira ga gwamnati da ta gina mana magudunan ruwa. Sai mun yi amfani da kwale-kwale sannan muke zuwa gidajenmu."

- Wata mata

Ambaliyar ruwa ta lalata gonaki

A wani labarin kuma, kun ji cewa ambaliyar ruwa ta lalata amfanin gonakin al'umma a karamar hukumar Argungu da wasu yankunan da dama a jihohin Kebbi da Neja.

Shugaban sashin hulɗa da jama’a na Hukumar bunƙasa wutar lantarki ta ƙasa (N-HYPPADEC), Nura Wakili ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, 27 ga watan Agustan 2024.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng