"Sun Zama Maboyar Miyagu:" FCTA Ta Bayar da Wa'adin Kammala Gine Gine a Abuja

"Sun Zama Maboyar Miyagu:" FCTA Ta Bayar da Wa'adin Kammala Gine Gine a Abuja

  • Hukumar gudanarwar babban birnin tarayya Abuja ta ce za ta fara rushe wasu gine-gine da mamallakansu su ka ki kammalawa
  • A wata sanarwa da wani jami'in FCTA, Felix Obuah ya sanyawa hannu, ya ce an ba masu gine-ginen da ba a karasa ba wa'adin karasawa
  • Ya bayyana dalilin da ya sa aka dauki matakin, wanda a cewarsa ya jibanci kyautata tsaron rayuka da dukiyoyin mazauna Abuja

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

FCT, Abuja - Hukumar gudanarwar birnin tarayya Abuja ta ba mutanen da ke da gidajen da ba a kammala ba wa’adin watanni uku su kammala su.

Hukumar ta yi barazanar rushe dukkanin wani gida da aka ki kammala shi a kwaryar birnin babban birnin tarayyar a wannan lokaci.

Kara karanta wannan

An shiga tashin hankali a Abuja, 'yan ta'adda sun kashe babban jami'in gwamnati

Abuja
FCTA ta bayar da wa'adin kammala kango a Abuja Hoto: Nyesom Ezenwo Wike/Abuja City
Source: Facebook

Punch ta wallafa cewa umarnin mai kunshe da wa'adin kammala kwangayen na kunshe a wata sanarwa da jami’in hukumar FCTA, Felix Obuah ya fitar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An gano karuwar kwangaye a Abuja

Jaridar Daily Trust ta tattaro cewa hukumar birnin tarayya Abuja ta ce an gano karuwar gine-gine da ba a kammala ba bisa ka’ida ba a birnin.

Jami’in hukumar FCTA, Felix Obuah ya bayyana cewa hakan ta sa aka ga dacewar bayar da lokacin ga mamallaka gidajen da su kammala su ko a ruguje su.

Abuja: Dalilin bayar da wa'adin kammala kwangayen

Hukumar gudanarwar Abuja ta ce gine-ginen da ba a kammala ba kan zama maboyar masu aikata miyagun laifuka a yankin.

"Hukumar ta gano cewa ana amfani da wadannan gine-gine da filaye wajen boye marasa gaskiya wanda ke zama babbar barazanar tsaro ga mazauna yankin," cewar Felix Obuah.

Kara karanta wannan

'Yana yawo cikin dare,' Sanata ya tona yadda Tinubu yake zagaya gari a boye

FCTA ta kaddamar da rushe gidaje a Abuja

A wani labarin kun ji cewa hukumar gudanarwar birnin tarayya Abuja ta bayyana cewa za ta fara rusa wasu daga cikin gidajen da aka gina a birnin ba bisa ka'ida ba domin tsaftace birnin.

Hukumar, karkashin jagorancin Ministan Abuja, Nyesom Wike ne ta bayyana cewa ba za ta lamunci a ci gaba da gina haramtattun gine-gine a sassan babban birnin Abuja ba.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano. aisha.ahmad@corp.legit.ng