"Sun Zama Maboyar Miyagu:" FCTA Ta Bayar da Wa'adin Kammala Gine Gine a Abuja

"Sun Zama Maboyar Miyagu:" FCTA Ta Bayar da Wa'adin Kammala Gine Gine a Abuja

  • Hukumar gudanarwar babban birnin tarayya Abuja ta ce za ta fara rushe wasu gine-gine da mamallakansu su ka ki kammalawa
  • A wata sanarwa da wani jami'in FCTA, Felix Obuah ya sanyawa hannu, ya ce an ba masu gine-ginen da ba a karasa ba wa'adin karasawa
  • Ya bayyana dalilin da ya sa aka dauki matakin, wanda a cewarsa ya jibanci kyautata tsaron rayuka da dukiyoyin mazauna Abuja

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

FCT, Abuja - Hukumar gudanarwar birnin tarayya Abuja ta ba mutanen da ke da gidajen da ba a kammala ba wa’adin watanni uku su kammala su.

Kara karanta wannan

An shiga tashin hankali a Abuja, 'yan ta'adda sun kashe babban jami'in gwamnati

Hukumar ta yi barazanar rushe dukkanin wani gida da aka ki kammala shi a kwaryar birnin babban birnin tarayyar a wannan lokaci.

Abuja
FCTA ta bayar da wa'adin kammala kango a Abuja Hoto: Nyesom Ezenwo Wike/Abuja City
Asali: Facebook

Punch ta wallafa cewa umarnin mai kunshe da wa'adin kammala kwangayen na kunshe a wata sanarwa da jami’in hukumar FCTA, Felix Obuah ya fitar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An gano karuwar kwangaye a Abuja

Jaridar Daily Trust ta tattaro cewa hukumar birnin tarayya Abuja ta ce an gano karuwar gine-gine da ba a kammala ba bisa ka’ida ba a birnin.

Jami’in hukumar FCTA, Felix Obuah ya bayyana cewa hakan ta sa aka ga dacewar bayar da lokacin ga mamallaka gidajen da su kammala su ko a ruguje su.

Abuja: Dalilin bayar da wa'adin kammala kwangayen

Hukumar gudanarwar Abuja ta ce gine-ginen da ba a kammala ba kan zama maboyar masu aikata miyagun laifuka a yankin.

Kara karanta wannan

'Yana yawo cikin dare,' Sanata ya tona yadda Tinubu yake zagaya gari a boye

"Hukumar ta gano cewa ana amfani da wadannan gine-gine da filaye wajen boye marasa gaskiya wanda ke zama babbar barazanar tsaro ga mazauna yankin," cewar Felix Obuah.

FCTA ta kaddamar da rushe gidaje a Abuja

A wani labarin kun ji cewa hukumar gudanarwar birnin tarayya Abuja ta bayyana cewa za ta fara rusa wasu daga cikin gidajen da aka gina a birnin ba bisa ka'ida ba domin tsaftace birnin.

Hukumar, karkashin jagorancin Ministan Abuja, Nyesom Wike ne ta bayyana cewa ba za ta lamunci a ci gaba da gina haramtattun gine-gine a sassan babban birnin Abuja ba.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.