Gwamna a Arewa Ya Hango Haɗari, Ya Rufe Manyan Makarantun Kudi Nan Take

Gwamna a Arewa Ya Hango Haɗari, Ya Rufe Manyan Makarantun Kudi Nan Take

  • Mai girma Dikko Umaru Radda ya ba da umarnin soke lasisi da rijistar makarantun lafiya na kuɗi a faɗin jihar Katsina
  • Gwamnan ya ce bincike ya nuna galibin makarantun lafiya masu zaman kansu ba su da inganci wanda hakan haɗari ne ga lafiyar jama'a
  • Mai taimakawa gwamnan kan harkokin lafiya, Umar Mammada ya ce wannan umarni zai fara aiki nan take har sai an gama bincike

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Katsina - Gwamna Malam Dikko Umaru Raɗɗa ya ba da umarnin rufe dukkan makarantun kiwon lafiya masu zaman kansu da ke aiki a faɗin jihar Katsina.

Mai ba gwamna shawara na musamman kan harkokin lafiya, Umar Mammada ne ya sanar da hakan a wata hira da manema labarai ranar Litinin a Katsina.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Tinubu ta yi wa ƴan Najeriya albashir da ASUU ke shirin rufe jami'o'i

Gwamnan Katsina, Dikko Radda.
Gwamna Dikko Radda ya rufe dukkan makarantun lafiya masu zaman kansu a Katsina Hoto: Dr. Dikko Umaru Radda
Asali: Facebook

A rahoton Punch, Umar ya ce gwamnatin Katsina ta gano cewa an samu karuwar makarantun horas da malaman lafiya marasa inganci a ƴan shekarun nan.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Binciken da gwamnati ta yi ta hannun ma'aikatar lafiya ya nuna akwai damuwa kan yadda wasu makarantun lafiya na kudi ke tafiyar da aikinsu ba tare da yin rijista ba.
"Wasu daga cikin ire-iren waɗannan makarantu ba su cika ƙa'idojin doka na fara aiki a matsayin makarantun koyar da aikin lafiya ba, wanda hakan ba karamin haɗari ba ne ga rayuwar jama'a.
"Bisa la'akari da haka ne Mai girma gwamna ya bayar da umarnin rufewa tare da soke rajista da lasisin dukkan makarantun kiwon lafiya na kudi a Katsina."

- Umar Mammada.

Ku saurari ƙarin bayani...

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262