Wike Ya Sake Nuna Yatsa ga Gwamnan PDP da Suke Takun Saka

Wike Ya Sake Nuna Yatsa ga Gwamnan PDP da Suke Takun Saka

  • Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Ezenwo Wike ya yi kakkausar suka ga magajinsa gwamnan jihar Rivers, Sir Siminalayi Fubara
  • Wike ya caccaki gwamnan ne kan wasu kalamai da ya yi na rashin mutuntawa ga wasu manyan lauyoyi
  • Ministann ya kuma gargaɗi masu son ganin an hukunta shi a jam'iyyar PDP kan su shiga taitayinsu domin shi ba kanwar lasa ba ce

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Rivers - Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya caccaki magajinsa kuma gwamnan jihar Rivers, Sir Siminialayi Fubara.

Wike ya caccaki Fubara ne kan wasu kalamai na rashin mutuntawa da ya yi a kwanakin baya kan wasu manyan lauyoyi.

Wike ya caccaki Gwamna Fubara
Wike ya caccaki Gwamna Fubara na Rivers Hoto: Sir Siminalayi Fubara, Nyesom Ezenwo Wike - CON, GSSRS
Asali: Facebook

Wike ya caccaki Fubara

Kara karanta wannan

‘Yan APC da suka koma kuka da gwamnati saboda tsadar rayuwa a zamanin Tinubu

Wike ya soki gwamnan ne a wajen wani taro da aka gudanar a jihar Rivers a ranar Asabar, 19 ga watan Oktoban 2024, cewar rahoton jaridar The Nation.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ministan ya nuna rashin jin daɗinsa kan yadda gwamnan ya yi rashin kyautatawa ga wasu manyan mutane uku a jihar waɗanda suka kai ruwa rana wajen ganin an zaɓe shi ya zama gwamna.

Wike ya ɗaga yatsa ga masu adawa da shi

Wike ya kuma yi kakkausar suka ga masu son ganin an hukunta shi a jam'iyyar PDP, inda ya ce suna ginawa kansu ramin mugunta ne.

"Ba mu fara ba. Za mu iya kuma a shirye muke."
"Duba mutanen da suke magana akan dakatar da ni. Rivers kadara ce kuma ba za mu taɓa zuwa mu rusuna muku ba. Idan baku san cewa Rivers kadara ba ce, idan kun isa ku yi abin da za ku yi daga inda kuke."

Kara karanta wannan

Kano: Muhimman abubuwa 5 game da kwamishinan da aka kama da zargin lalata da matar aure

- Nyesom Wike

Karanta wasu labaran kan rikicin Rivers

Wike ya caccaki Atiku

A wani labarin kuma, kun ji cewa ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya caccaki tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar shugaban kasa a zaben 2023 a PDP, Atiku Abubakar.

Wike ya bayyana cewa ƴan Najeriya sun ki jinin Atiku, bayan da ya tsaya takara a zaben shugaban kasa kuma ya fadi “sau da yawa” a tarihin siyasarsa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng