Sarki Sanusi II Ya Nada Kawun Gwamna Abba Kabir Yusuf Babban Matsayi a Masarautar Kano

Sarki Sanusi II Ya Nada Kawun Gwamna Abba Kabir Yusuf Babban Matsayi a Masarautar Kano

  • Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya halarci taron nadin sarauta a fadar Mai Martaba Muhammadu Sanusi II
  • An nada kawun gwamna a matsayin Danmakwayon Kano, Abba ya yaba wa sarkin Kano na yanzu
  • Jihar Kano na daga cikin jihohin da Arewacin Najeriya ke alfahari da su, musamman ta fuskar masarauta

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Jihar Kano - An nada kawun gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf a matsayin Danmakwayon Kano a fadar Mai Martaba Sarki Muhammadu Sanusi II.

Sabon Danmakwayon Kano na yanzu shi ne Alhaji Abba Yusuf, wanda ya kasance kawun gwamna mai ci a jihar ta Kano.

Baya ga wannan, an kuma nada wasu sabbin hakimai guda shida na yankuna a jihar mai dogon tarihi.

An nada Kawun Abba Sarauta a Kano
Lokacin da ake bikin nada kawun Abba Kabir Yusuf | Hoto: Kyusufabba
Asali: Twitter

Nadin sarautar da aka yi a Kano

Da yake bayyana nadin da kuma halartar bikin nadin sarautar, gwamna Abba ya ce:

Kara karanta wannan

Kano: Ana so a raba shi da Kwankwaso, Gwamna Abba ya amince da ayyukan N36bn

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

“Na samu karamci a fadar Sarkin Kano na halartar bikin nadin sarautar hakimai guda shida, ciki har da kawuna, Alhaji Abba Yusuf a matsayin Danmakwayon Kano, sarautar da mahaifinsa da ya rasu ya rike.”

Abba ya yiwa Sarki Sanusi godiya

A bangare guda, gwamnan ya yiwa Sarkin Kano fatan alheri tare da bayyana amincin da aka samu a masarautar.

A cewarsa:

“Dole ne in yaba wa Mai Martaba, Khalifa Muhammadu Sanusi II, Sarkin Kano bisa tabbatar da daidaito a masarautar mai martaba.”

Allah ya dafawa sarakunan gargajiya, gwamna Abba

Daga karshe, gwamnan ya yiwa dukkan sarakunan gargajiya a jihar da kewaye fatan alheri, inda ya yi masu addu’ar Allah ya dafa masu.

“Allah Madaukakin Sarki Ya yi wa dukkan Sarakunan gargajiya na Kano jagora.”

Jihar Kano na daga cikin jihohin Arewacin Najeriya da ke dimbin tarihi, musamman a fannin sarauta da kasuwanci.

Kara karanta wannan

Rikicin APC ya ƙara ƙamari, babban basarake a Arewa ya yi murabus daga sarauta

Kalli hotunan da Abba ya yada:

Gwamna Abba ya yi kora a Kano Pillars

A wani labarin, gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya sanya hannu kan korar shugabannin rikon kwarya na kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars.

Shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin jihar, Shehu Wada Sagagi ne ya tabbatar da hakan a wata hira da manema labarai a jihar Kano.

A shekarun baya Kano Pillars na ɗaya daga cikin kungiyoyin da tauraruwarsu ke haskawa a gasar cin kofin firimiya na gida Najeriya, Leadership ta ruwaito.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.