An Shiga Duhu: Wutar Lantarkin Najeriya Ta Sake Rikicewa a Karo Na Uku Cikin Mako Guda

An Shiga Duhu: Wutar Lantarkin Najeriya Ta Sake Rikicewa a Karo Na Uku Cikin Mako Guda

  • Tsarin wutar lantarkin Najeriya ya sake birkicewa a karo na uku, inda 'yan Najeriya ke kukan duhu
  • A cikin mako guda, an samu daukewar wutar lantarki mai tsanani, inda 'yan Najeriya ke fuskantar asarar dukiya
  • Mai sana'ar fawa, Muhammad Adamu ya bayyanawa Legit irin asarar nama da ya yi a ranakun Litinin da Talata

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Najeriya - A karo na uku cikin mako guda, tsarin wutar lantarkin Najeriya ya sake birkicewa a ranar Asabar 19 ga watan Oktoba.

An daina samar da wutar lantarki a kasar tun da sanyin safiyar Asabar kusan karfe 8:16, kamar yadda rahotanni suka bayyana.

Yadda aka kuma dauke wuta a Najeriya
Yadda dauke wuta ya zama ruwan dare a Najeriya
Asali: Getty Images

Idan baku manta ba, a baya myn ruwaito cewa wutar lantarkin Najeriya ta dauke dif a ranakun Litinin da Talata.

Yadda matsalar take a wannan karon

Binciken jaridar Punch ya tabbatar da cewa an samar da megawatt 3,042 na wuta da misalin karfe 8 na safe, sannan ya kai kololuwar megawatt 3,968 da misalin karfe 7 na safe.

Kara karanta wannan

An barke da murna da kamfanin NNPCL da Chevron suka sake hako wata rijiyar mai

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sai dai, samar da wutar ya ragu zuwa megawatt 47 da misalin karfe 9 na safe, wanda ya nuna samuwar matsala ga tsarin wutar.

Ya zuwa lokacin hada wannan rahoton, isowar wuta ga kamfanonin rarraba wutar lantarki ya tsaya a megawatt 0.00.

Ba a samu tabbacin musabbabin cabewar tsarin ba a ya zuwa yanzu, domin ba a samu damar tattaunawa da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Najeriya ba.

Na yi asarar kusan rabin saniya

Wani mahauci da ke zaune a unguwar Bye Pass da ke Gombe, ya fadi irin asarar da ya yi bayan daukewar wuta.

A cewar Muhammad Adamu:

"Daukewar wutan nan ya taba ni, domin na dogara da ita don amfani da na'urar daskarar da abinci, amma ba a kawo ta ba.
"Haka na yi asarar kusan rabin saniya saboda na saka a na'urar da jiran za a kawo wuta, da ba a kawo ba kaya ya rube, haka na tattara na sayar, ban mayar da kudin ba."

Kara karanta wannan

Tsohon gwamna ya bayyana babbar matsalar Najeriya da Tinubu ya fara magancewa

Yadda ta kaya a makon jiya

A wani labarin, gwamnatin tarayya ta bayyana cewa dole a cigaba da samun matsalar wutar lantarki a fadin kasar nan, saboda wasu dalilai.

Ministan makamashin ya ce amma akwai hanyar da za a bi wajen magance matsalar yawaitar lalacewar turakun lantarki.

Ya zama ruwan dare a samu daukewar wutar lantarki a Najeriya, kuma hakan yana shafan kasuwancin 'yan kasar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.