Sojoji Sun Bindige 'Yan Bindigan da Suka Je Karbar Kudin Fansa

Sojoji Sun Bindige 'Yan Bindigan da Suka Je Karbar Kudin Fansa

  • Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar hallaka wasu ƴan bindiga mutum biyu har lahira a jihar Kaduna
  • Sojojin sun sheƙe ƴan bindigan ne lokacin da suka je ɗaukar kuɗin fansa na wasu mutum huɗu da aka dauke
  • Sojojin sun yi wa ƴan bindigan shigo-shigo ba zurfi ne wanda hakan ya sanya suka samu nasarar hallaka su

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Kaduna - Sojoji sun bindige wasu ƴan bindiga guda biyu a lokacin da suke ƙoƙarin karɓar kuɗin fansa a jihar Kaduna.

Ƴan bindigan dai sun je karɓar N1.5m a matsayin kudin fansar mutane huɗu da suka sace a ƙauyen Mai-Iddo da ke ƙaramar hukumar Kachia a jihar Kaduna.

Kara karanta wannan

Mutane kusan 100 sun rasu sakamakon fashewar tankar mai a Jigawa

Sojoji sun hallaka 'yan bindiga a Kaduna
Sojoji sun sheke 'yan bindiga a jihar Kaduna Hoto: Legit.ng
Asali: Original

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa sojojin sun kuɓutar da mutanen huɗu da suka haɗa da mata uku da yaro ɗaya, waɗanda aka yi garkuwa da su a wata gona a makon jiya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda sojoji suka kashe ƴan bindigan

Shugaban al’ummar yankin ya tabbatar da faruwar lamarin ta wayar tarho a ranar Talata, 15 ga watan Oktoban 2024.

Ya ce an kashe ƴan bindigan ne bayan shugabansu ya umarce su da su je wani wuri da aka tsara cewa ɗan uwan mutanen da aka sace zai ajiye kuɗin fansan.

"An kammala shirye-shirye tsakanin sojoji tare da mutumin da zai kai musu kuɗin fansa da kuma ɗan banga. Da isa wurin, sai sojojin suka ɓoye."
"Yayin da biyu daga cikin ƴan bindigan suka fito domin karɓar kudin fansan, sai sojojin suka buɗe musu wuta tare da hallaka su nan take."

Kara karanta wannan

Jagororin APC sun ba 'yan Najeriya shawara kan gwamnatin Tinubu

- Wani shugaban al'umma

Ya ƙara da cewa sojojin sun kuɓutar da mutanen da aka yi garkuwa da su tare da sake haɗa su da iyalansu.

Wane bayani ƴan sanda suka yi?

Ba a samu jin ta bakin kakakin rundunar ƴan sandan jihar Kaduna, ASP Mansur Hassan wannan lamarin ba.

Kakakin ƴan sandan bai ɗauki kiran wayar da aka yi masa ba sannan bai dawo da amsar saƙon da aka tura masa ba har zuwa lokacin kammala haɗa wannan rahoton.

Ƴan bindiga sun harbi shugaban rundunar tsaro

A wani labarin kuma, kun ji cewa wasu ƴan bindiga sun harbi darakta janar na rundunar Askawaran Zamfara (CPG), Janar Lawal B. Muhammad (mai ritaya).

Ƴan bindigan sun harbi Janar Muhammad ne a lokacin da suka kai hari kan masu ababen hawa a ƙauyen Kucheri da ke ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng