IGP Ya Tuna da Iyalan 'Yan Sandan Kano da Suka Rasu a Hatsarin Mota

IGP Ya Tuna da Iyalan 'Yan Sandan Kano da Suka Rasu a Hatsarin Mota

  • IGP Kayode Egbetokun ya ba da diyya ga iyalan ƴan sandan da suka rasu sakamakon hatsarin mota a jihar Kano
  • Sufeto Janar na ƴan sandan ya ba da diyyar N10m ga iyalan waɗanda suka rasu tare da N2m ga jani'an da suke jinya a asibiti
  • Jami'an ƴan sandan dai sun yi hatsarin ne lokacin da suke kan hanyar dawowa daga zaɓen gwamnan jihar Edo

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - IGP Kayode Egbetokun ya amince da biyan diyyar Naira miliyan 10 ga iyalan jami’an ƴan sanda biyar da suka rasa rayukansu a wani hatsarin mota.

Jami’an sun dawo ne daga zaɓen gwamnan Edo a watan Satumba, lokacin da motarsu ta yi hatsari a garin Karfi da ke ƙaramar hukumar Kura ta jihar Kano.

Kara karanta wannan

Sojoji sun yi artabu da 'yan bindiga, an samu asarar rayuka masu yawa

IGP ya ba da diyyar N10m
IGP ya ba da diyya ga iyalan 'yan sandan da suka rasu a Kano Hoto: Nigeria Police Force
Asali: Twitter

Kakakin rundunar ƴan sandan Najeriya, Olumuyiwa Adejobi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba, a shafin X.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Olumuyiwa Adejobi ya bayyana cewa an sallami takwas daga cikin jami’an 11 da suka samu raunuka a hatsarin, yayin sauran guda uku ke kwance a asibiti.

IGP ya ba da diyyar N10m

Kakakin ya ce Kayode Egbetokun ya kuma amince da biyan N2m ga waɗanda har yanzu ke kwance a asibiti, da kuma N500,000 ga waɗanda aka sallama.

"Sufeto Janar na ƴan sanda ya ɗauki matakin bayar da tallafi ga waɗanda abin ya shafa, ta hanyar amincewa da biyan diyyar Naira Miliyan Goma (N10,000,000) ga iyalan waɗanda suka rasu."
"IGP ya kuma amince da biyan N2m ga waɗanda har yanzu suke kwance a asibiti domin samun cikakkiyar kulawa yayin da suke jinya jinya, da kuma N500,000 ga waɗanda aka sallama."

Kara karanta wannan

Bayan Sarkin Gobir, wani Basarake ya sake rasuwa a hannun 'yan bindiga

- Olomuyiwa Adejobi

IGP ya janye ƴan sanda a Rivers

A wani labarin kuma, kun ji Sufeto Janar na ƴan sandan Najeriya (IGP), Kayode Egbetokun, ya bayar da umarnin janye ƴan sanda daga sakatariyoyin ƙananan hukumomi 23 na jihar Rivers

Umarnin janye ƴan sandan na zuwa ne bayan Gwamna Siminalayi Fubara na jihar ya rantsar da zaɓaɓɓun shugabannin ƙananan hukumomi.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng