Badakalar N27bn: EFCC Ta Sa Lokacin Gurfanar da Tsohon Gwamna a gaban Kotu
- Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC ta shirya gurfanar da tsohon gwamnan jihar Taraba a gaban kotu
- Majiyoyi daga hukumar sun bayyana cewa za a gurfanar da Darius Ishaku a gaban kotu a ranar Litinin kan badaƙalar N27bn
- Jami'an hukumar EFCC dai sun cafke tsohon gwamnan ne a gidansa da ke birnin tarayya Abuja a ranar Juma'a
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
FCT, Abuja - Hukumar yaƙi da masu yiwa tattalin arziƙin ƙasa zagon ƙasa (EFCC) na iya gurfanar da tsohon gwamnan jihar Taraba, Darius Ishaku a gaban kotu bisa zargin almundahanar N27bn a ranar Litinin.
Majiyoyi daga EFCC sun bayyana cewa Darius Ishaku, wanda ke da haƙƙin samun beli idan ya cika sharuɗɗan EFCC, zai gurfana a kotu ranar Litinin.

Asali: Twitter
EFCC ta dade tana bibiyar Darius Ishaku
Jaridar Leadership ta ce majiyar ta ce hukumar ta EFCC ta shafe shekaru tana bin diddigin tsohon gwamnan kuma tana da tuhume-tuhume masu ƙarfi a kansa.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Jami’an hukumar EFCC sun cafke Darius Ishaku a ranar Juma’a a gidansa da ke Abuja.
Kakakin hukumar, Dele Oyewale, wanda ya tabbatar da kamun, ya ƙi yarda ya yi ƙarin bayani a kai, rahoton jaridar Premium Times ya tabbatar.
Majiyoyi daga EFCC sun ce har yanzu tsohon gwamnan na hannun hukumar har zuwa lokacin kammala haɗa wannan rahoton.
Me ake tuhumarsa a kai?
Majiyar ta ƙara da cewa an shigar da tuhume-tuhume aƙalla 15 a kan tsohon gwamnan kuma za a gurfanar da shi a gaban kotu domin an tattara shaidu a kansa.
Darius Ishaku, wanda ya bar mulki a shekarar 2023 bayan ya yi gwamna na tsawon shekaru takwas, an cafke shi a gidansa da ke Abuja da safiyar ranar Juma’a.

Kara karanta wannan
Arewa na cikin matsala, ambaliya ta ƙara kashe mutum 29, gidaje 321,000 sun lalace
"Eh, yana hannunmu a yanzu. Tun bayan tafiyarsa a matsayin gwamnan jihar muna ta bincikensa a ɓoye. Ya yi ta’ammali da kuɗi masu yawa."
- Wata majiya
EFCC ta ƙalubalanci tsohon gwamna
A wani labarin kuma, kun ji cewa hukumar yaƙi da yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC) ta ce a shirye ta ke wajen fuskantar tsohon gwamnan Kogi, Bello Yahaya a kotu.
Jami'in hulda da jama'a na hukumar EFCC, Dele Oyewale ya ce dole sai Yahaya Bello ya fuskanci alƙali kan zargin da ake yi masa.
Asali: Legit.ng