Murnar Samun 'Yan Cin Kai: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Hutu

Murnar Samun 'Yan Cin Kai: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Hutu

  • Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ba da hutu domin bikin murnar zagayowar da ƙasar nan ta samu ƴancin kai daga hannun turawan mulkin mallaka
  • Gwamnatin ta ayyana ranar Talata, 1 ga watan Oktoba a matsayin ranar hutu domin murnar cika shekara 64 da samun ƴancin kai
  • Ministan harkokin cikin gida wanda ya sanar da hakan a madadin gwamnatin tarayya ya taya ƴan Najeriya murnar zagayowar lokacin

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Gwamnatin tarayya ta ba da hutu domin murnar zagayowar ranar samun ƴancin kan Najeriya.

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Talata, 1 ga watan Oktoban 2024 a matsayin ranar hutu domin bikin cikar Najeriya shekara 64 da samun ƴancin kai.

Gwamnatin tarayya ta ba da hutu
Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Talata a matsayin ranar hutu Hoto: Dr. Olabunmi Tunji-Ojo
Asali: Facebook

Gwamnatin tarayya ta ba da hutu

Kara karanta wannan

Shirin zanga zanga a watan Oktoba ya girgiza gwamnatin Tinubu, an fara lallaɓa matasa

Babban sakatare a ma'aikatar cikin gida Dr Magdalene Ajani ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa a ranar Asabar a shafin X na ma'aikatar harkokin cikin gida.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya bayyana cewa ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ya ayyana ranar hutun ne a madadin gwamnatin tarayya.

Ministan ya taya ƴan Najeriya na cikin gida da ƙasashen waje murnar zagoyawor lokacin.

Dr. Olabunmi Tunji-Ojo ya kuma yaba da haƙuri da jajircewar ƴan Najeriya, inda ya bayyana cewa sadaukarwar da suke yi ba za ta tafi a banza ba.

"Yayin da yake taya ƴan Najeriya murnar zagayowar ranar samun ƴancin kai, Dr. Olabunmi Tunji-Ojo ya buƙace da su ci gaba da jajircewa wajen gina ƙasa."

Dr. Magdalene Ajani

A ranar, 1 ga watan Oktoban 1960 ne dai Najeriya ta samu ƴancin kai daga hannun ƙasar Ingila.

Kara karanta wannan

Arewa na cikin matsala, ambaliya ta ƙara kashe mutum 29, gidaje 321,000 sun lalace

Gwamnoni sun ba da hutu

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnatocin jihohin Legas, Osun, Oyo da Ogun sun ayyana Talata 20 ga watan Agusta a matsayin ranar hutu domin tunawa da Ranar Isese.

Bayanin ba da hutun na kunshe ne a cikin wasu sanarwa daban-daban da kwamishinonin yada labarai na kowace jiha suka fitar.

Ranar Isese tana nufin nau'ikan bukukuwan al'adun da Yarabawa ke gudanarwa a Najeriya da Cuba, Brazil, Amurka, Benin, da sauran ƙasashe

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng