"An Samu Canji": Hukumar Alhazai, NAHCON Ta Sanar da Sabon Tsarin Aikin Hajjin 2025

"An Samu Canji": Hukumar Alhazai, NAHCON Ta Sanar da Sabon Tsarin Aikin Hajjin 2025

  • NAHCON ta sanar da wani sabon tsari da hukumomin ƙasar Saudiyya suka kawo wanda za a fara aiwatarwa a hajjin 2025
  • Mai magana da yawun hukumar NAHCON, Fatima Usara ta ce daga yanzu ciyarwa da ɗakunan kwanan alhazai sun koma hannun Saudiyya
  • Ta ce tuni shirye-shiryen hajjin baɗi suka yi nisa kuma hukumar ta zauna da wakilan jihohi kan wannan sabon tsari

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Hukumar jin daɗin alhazai ta ƙasa watau NAHCON ta sanar da wasu canje-canje da aka samu a aikin hajjin da za a yi idan Allah ya kaimu baɗi 2025.

NAHCON ta bayyana cewa hukumomin kasar Saudiyya za su karɓi ragamar ciyarwa da ɗakunan kwanan alhazai a Makkah a Madinah.

Kara karanta wannan

Arewa na cikin matsala, ambaliya ta ƙara kashe mutum 29, gidaje 321,000 sun lalace

Alhazai a ƙasa mai tsarki.
Hukumar jin daɗin alhazai NAHCON ta ce Saudiyya ta ɓullo da sabon tsari a hajjin 2025 Hoto: Inside The Haramain
Asali: Facebook

Premium Times ta ruwaito cewa hakan na kunshe ne a wata sanarwa da mai magana da yawun NAHCON, Fatima Sanda Usara ta fitar ranar Jumu'a.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

NAHCON ta fara shirin hajjin 2025

Fatima Usara ta ce an amince da sabon tsarin ne a yayin wani taro ta intanet tsakanin hukumar da ma'aikatar aikin Hajji da Umrah ta Saudiyya (MoHU).

Ta kuma tabbatar da cewa shirye-shiryen hajjin 2025 sun yi nisa kuma hukumar ta zauna da shugabannin hukumomin jin daɗin alhazai na jihohi ranar 23 ga watan Satumba.

Fatima ta ce a wannan zama, kwamishinan sashin ayyuka na NAHCON, Anofi Olanrewaju-Elegushi ya sanar da jihohi tsarin da Saudiyya ta ɓullo da shi.

Saudiyya ta kawo sabon tsari a hajjin 2025

Kakakin NAHCON ta haƙaito kwamishinan na cewa kamafanonin kula da mahajjata da aka fi sani ma'assasa za su karɓi ragamar ciyarwa da ɗakunan kwanan alhazai a Makkah da Madinah.

Kara karanta wannan

Ana zaman makoki a Borno: Ambaliya ta halaka mutane 11, ta lalata kadarori a Neja

A ruwayar Guardian, kwamishinan NAHCON ya ce:

"Wannan tsarin zai shafi kowace ƙasa za ta tura mutanenta hajji kuma za a fara aiwatar da shi ne daga alhazan baɗi 2025.
"Kun sani dai a baya ma'aikatar aikin Hajji da Umrah ta Saudiyya MoHU ta gabatar da shawarar ɗaukar nauyin ciyarwa a Masha’ir a 2022, kuma a shekarar aka aiwatar."

EFCC ta saki tsohon shugaban NAHCON

A wani rahoton kuma hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya ta bayar da belin tsohon shugaban NAHCON da sakatarensa.

EFCC ta saki Jalal Arabi tare da Abdullahi Kontagora bayan sun cika sharuɗɗan belinsu a hannun hukumar yaki da rashin gaskiyar

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262