Wata Tanka Maƙare da Man Fetur Ta Fashe, Ta Yi Wa Mutane Illa a Abuja

Wata Tanka Maƙare da Man Fetur Ta Fashe, Ta Yi Wa Mutane Illa a Abuja

  • Wata tanka maƙare da man fetur ta fashe a kan dogon titin Maitama da ke babban birnin tarayya Abuja ranar Litinin, 23 ga watan Satumba
  • Rahotanni sun nuna cewa wuta ta kama sosai bayan fashewar tankar, lamarin da ya sa mutane guduwa domin neman tsira da rayuwarsu
  • Wani ma'aikaci a ɗaya daga cikin asibitocin Maitama ya bayyana cewa an kawo waɗanda lamarin ya rutsa da su domin ba su kulawa da yi masu magani

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Wata babbar tanka maƙare da man fetur ta fashe ta kama da wuta a Maitama, ɗaya daga cikin manyan unguwanni a babban birnin tarayya Abuja.

Bayanai sun nuna wasu mutane da ke cikin motar haya a kusa da tankar sun samu raunuka daban-daban sakamakon fashewar yau Litinin, 23 ga watan Satumba.

Kara karanta wannan

Tinubu ya shiga taron FEC ana rade raɗin za a kori wasu ministoci, bayanai sun fito

Taswirar Abuja.
Mutane da dama sun jikkata da wata tanka maƙare da man fetur ta yi bindiga a Abuja Hoto: Legit.ng
Asali: Original

Jaridar Daily Trust ta tattaro cewa lamarin ya faru ne a titin Shehu Shagari, Maitama a babban birnin Najeriya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda tankar ta fashe ta kama da wuta

Wani ganau, Saminu Sani ya bayyana cewa bayan fashewar tankar, sun ga harshen wutar da ta kama ya yi tsini a sararin samaniya.

Ya ce galibin masu ababen hawa sun bar motocinsu a kan titi, sun gudu domin tsira da rayuwarsu daga wutar da ta tashi mai tsananin zafi.

Saminu ya ƙara da cewa lamarin ya haifar da cunkoso a ttitin wanda ya shafi wurare da dama kamar farmers market, Nicon Hilton Hotel, MTN da Chicken house.

Fashewar tankar ya raunata mutane

Wani jami'in lafiya a asibitin da ya fi kusa da wurin a Maitama ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce an kawo masu mutanen da suka ji raunuka a fashewar tankar.

Kara karanta wannan

Edo 2024: Ana tsaka da kada kuri'a, 'yan bindiga sun yi awon gaba da akwatin zabe

Mutumin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce ya ji wasu daga cikin waɗanda ibtila'in ya rutsa da su na cewa direban tankar da ta fashe ya gudu.

Gobara ta laƙume dukiya a Legas

A wani rahoton kuma mutane da dama sun tafka asara bayan gobara ta tashi a kasuwar katako ta Itamaga a Ikorodu da ke jihar Lagos.

Daraktan hukumar ba da agajin gaggawa, Nosa Okunbor ya ce gobarar ta jawo mummunan asara na miliyoyi a jihar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262