Ana Wahalar Rayuwa, Gwamna a Arewa Ya Ware N22bn domin Aikin Samar da Ruwa

Ana Wahalar Rayuwa, Gwamna a Arewa Ya Ware N22bn domin Aikin Samar da Ruwa

  • Gwamnatin Katsina ta ware kuɗi N22bn domin aikin samar da wadataccen ruwan sha a faɗin kananan hukumomi 34
  • Shugaban hukumar ruwa ta Katsina, Tlllle ya bayyana hakan, ya ce aikin zai kawo ƙarshen ƙarancin ruwa da rashin tsaftarsa
  • Wannan aiki za a yi shi karkashin kulawar wani shiri na haɗin guiwa tsakanin gwamnatin Katsina da bankin duniya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Katsina - Gwamnatin Katsina karkashin jagorancin Malam Dikko Umaru Raɗɗa ta ware N22bn domin aikin samar da ruwa a faɗin kananan hukumomi 34.

Gwamnatin ta ce ta ware waɗannan maƙudan kuɗi ne domin tabbatar da samar da ruwan sha mai tsafta ga al'ummar jihar Katsina.

Kara karanta wannan

Kumallon mata: Wata matar aure a Kano ta zuba 'fiya fiya' a abincin ɗan kishiyarta

Malam Dikko Radda.
Gwamnatin Katsina ta zuba Naira biliyan 22 a aikin samar da ruwa Hoto: Dr. Dikko Umaru Radda
Asali: Facebook

Manajan Datakta na hukumar ruwa ta Katsina, Tukur Hassan ne ya bayyana hakan ranar Laraba, kamar yadda Leadership ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ƙarancin ruwa zai zama tarihi a Katsina

A cewarsa, suna sa ran wannan aikin zai kawo ƙarshen kalubalen ƙarancin ruwa da rashin tsaftar ruwan sha a faɗin jihar.

Tukur Hassan ya ce:

"Muna da manyan ƙalubale guda biyu waɗanda muke ƙoƙarin shawo kansu a yanzu. A farko akwai bukatar mu fahimci wannan aiki da aka kinkimo, kusan mun gama da wannan batu."
"Haka nan kuma duk wani aikin (ruwa) da aka yi a wani wuri, ana bukatar al'ummar wannan yankin su kula da shi domin ya ɗore."

Aikin zai gudana a ƙarƙashin SURWASH

Shugaban sashen ayyukan samar da ruwan sha na shirin SURWASH, Aminu Dayabu ya ce hukumar za ta karbi N17bn daga cikin kuɗin da gwamnati ta ware don fara aikin.

Kara karanta wannan

Gwamna ya bi sahun takwarorinsa a shirin fara biyan ma'aikata sabon albashin N70,000

Ya bayyana amfanin wannan aiki a rayuwar mutane, yana mai nuni da tsare-tsare da ka’idojin da gwamnati ta shinfiɗa domin aikin ya gudana a lungu da saƙon Katsina.

SURWASH wani shiri ne na hadin gwiwa ne tsakanin gwamnatin Katsina da bankin duniya don samar da ruwa ga al'ummar jihar, rahoton Katsina Post.

Gwamnatin Katsina ta tura tallafi ga Borno

Kuna da labarin Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda ya hada tawaga mai karfi zuwa jihar Borno domin jajanta musu a kan ambaliyar ruwa.

An ruwaito cewa tawagar ta hada da mai martaba Sarki Daura, kakakin majalisar jihar da wasu jami'an gwamnatin Katsina.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262