Dubu Ta Cika: An Kama Wani Dattijo Ɗan Shekara 74 Yana Sata a Masallaci

Dubu Ta Cika: An Kama Wani Dattijo Ɗan Shekara 74 Yana Sata a Masallaci

  • Jama'a sun yi ram da wani ɗattijo ɗan shekara 74 wanda ke sace masu tabarmin masallacin unguwa a Rigasa, ƙaramar hukumar Igabi a Kaduna
  • Mutumin mai suna Jibril Musa ya amsa laifinsa, inda ya ce ya jima yana ƴan ɗauke-ɗauke a masallatai amma bai taɓa satar Alƙur'ani ba
  • Jibril da ake zargi da laifin satar, ya bayyana hanyar da yake bi wajen satar, ya ce yana sayar da duk tabarma ɗaya a kan N1,500 zuwa N2,000

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kaduna - Dubun wani dattijo ɗan shekara 74 a duniya, Jibril Musa da ke yawan sace-sace a Masallaci ya cika a unguwar Rigasa da ke ƙaramar hukumar Igabi a Kaduna.

Kara karanta wannan

Tsohon mataimakin shugaban APC ya yi hasashen makomar Shugaba Tinubu a 2027

Mazauna unguwar sun kama dattijon dumu-dumu yana satar tabarmun Masallacin da suke yin sallolin farilla.

Taswirar Kaduna.
Jama'ar Unguwa sun kama ɓarayon tabarmin masallaci a Kaduna Hoto: Legit.ng
Asali: Original

Kamar yadda jaridar Daily Trust ta rahoto, lamarin ya faru ne a layin Sarkin Bori Sule, inda mutane suka cafke dattijon kuma bai musa ba, ya masa laifinsa.

Kaduna: Yadda ɓarawon ya addabi Masallatai

Rahotanni sun bayyana cewa mazauna unguwar sun jima suna ƙorafin yawan sace-sacen tabarmi a Masallaci, hakan ya sa suka fara sa ido domin gano ɓarayon.

Bayan cafke shi, Jibiril Musa ya amsa laifinsa da cewa ya jima yana ɗauke-ɗauken tabarmi a Masallatai daban-daban a unguwar.

Ya kuma yi bayanin cewa wannan shi ne karo na biyu da ya saci tabarma a wannan Masallacin, kuma aka kama shi.

Dattijon da aka kama ya yi bayani

Da yake bayanin yadda yake fakar ido ya sace tabarmi, Jibril Musa ya ce:

Kara karanta wannan

Borno: Mutanen Maiduguri sun wayi gari da labari mai daɗi bayan ambaliyar da ta afku

"An kama ni da tabarmar da na sato a masallacin. Yadda nake yi shi ne, zan je sallar jam'i, idan mutane suka gama suka fita sai na kwashe sababbin tabarmu.
"Wasu lokutan na kan jira har sai kowa ya fita masallacin ya zama ba kowa sannan na kwashe tabarmun, wannan ne karo na biyu da na zo nan masallacin.
"Ina sayar da duk tabarma ɗaya da na sato kan N1,500 zuwa N2,000."

Dattijon ya bayyana cewa wani lokacin ya kan sace agogon Masallaci amma bai taɓa satar Alƙur'ani Mai Tsarki ba.

Kaduna: Ambaliya ta rusa gada

A wani rahoton kuma ambaliyar ruwa da ruguza gadar da ta haɗa garin Saminaka da wasu kauyukan manoma biyar a ƙaramar hukumar Lere ta Kaduna.

Kwamitin ambaliyar ruwa da Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani ya kafa ya kai ziyara yankin domin duba ɓarnar da ruwan ya yi.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262