Gwamna Ya Ɗauki Zafi kan Yan Bindiga, Ya Bukaci Malamai Su Faɗi Sakon Manzon Allah

Gwamna Ya Ɗauki Zafi kan Yan Bindiga, Ya Bukaci Malamai Su Faɗi Sakon Manzon Allah

  • Malam Dikko Umaru Radɗa ya buƙaci mutanen Katsina su tashi su kare mutuncin su da na iyalansu daga hare-haren ƴann bindiga
  • Gwamna Dikko Raɗɗa ya buƙaci malamai su isar da saƙon Allah da Manzonsa game da matakin da ya kamata mutane su ɗauka kan ɓarayi
  • Radda ya ce gara mutuwa da mutum ya tsaya a gabansa wasu ƙatti su kwanta da matarsa da ɗiyarsa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Katsina -Gwamn Malam Dikko Umaru Radda, ya yi kira ga al’ummar jihar Katsina su dauki matakan kare kansu daga hare-haren ‘yan bindiga.

Ya yi wannan kiran ne a wata ziyara da ya kai shiyyar Daura domin tattaunawa da al'umma kan abubuwan da suke bukatar gwamnati ta yi a kasafin kuɗin 2025.

Kara karanta wannan

Gwamna ya fallasa yadda shugaban al'umma ya karbi kudi aka hallaka mutane a yankinsa

Malam Dikko Radda.
Gwamnan Katsina ya sake kira ga al'umma su tashi tsaye su kare kansu daga hare-haren ƴan bindiga Hoto: Dr. Dikko Umaru Radda
Asali: Twitter

Gwamna ya roki malamai su faɗar da mutane

Daily Trust ta ce Radda ya bukaci malaman addinin Musulunci da su fadakar da mutane game da muhimmancin kare kai kamar yadda Musulunci ya tanada.

Gwamnan, wanda ya nuna damuwarsa a fili, ya ce abin takaici ne wasu tsirarun ƴan bindiga su shiga gari guda, amma mutane su bari su ci mutuncinsu.

A cewarsa, bai dace a ce busassun ƴan bindiga uku da yunwa ta masu katutu za su tasa mutum 1,000 ba yayin da sauran jama'a ke jin tsoro wasu su ɓoye a karƙashin gado.

Gwamna Raɗɗa ya bukaci a kare kai

"Ga malamanmu a nan, ya zama dole a kansu su isar da saƙon Manzon Allah (SAW) game da ɓarayon da ya zo farautar rayuwarka ko dukiya. Me Allah ya ce ka yi?"

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun yi ta'asa a wani harin ta'addanci a Katsina

"Wane irin lalacewa ce ka tsaya kana kallo wasu su yi amfani da matarka da ɗiyarka? Ina amfanin rayuwarka? Gara mutuwa da irin wannan wulaƙancin."
"Suna tsoron kauyukan da suka san mutane na tunkararsu, ba su zuwa waɗannan kauyukan, don haka dole mu tashi tsaye mu dakatar da kashe-kashen da ake mana, mu zauna cikin shiri."

- Dikko Radda.

Yadda mutane za su tari ƴan bindiga

Gwamnan ya ce idan ƴan bindiga 5 zuwa 10 suka shiga gari, matukar mutane 500 za su haɗu su tunkare su, to kafin ɗayansu ya kashe mutum 5 an murƙushe shi, Daily Post ta kawo.

Wannan dai ba shi ne karon farko da Gwamna Radda ya yi wannan kiran na mutane su kare kansu ba, ko a watan Fabrairu ya yi irin wannan kira.

Wani matashin Malami a yankin karamar hukumar Ɗanja, Malam Yahuza Bn Abdalla ya ce kalaman gwamna suna da tushe a Musulunci.

Kara karanta wannan

Jerin Sanatoci 10 da suke karɓan albashi na musamman duk wata a Majalisa

Malamin ya shaidawa Legit Hausa cewa:

"Duk wanda ya mutu wajen kare mutunci kansa, iyalansa da dukiyarsa ana sa ran ya yi shahada kamar yadda Manzon Allah SAW ya faɗa, saboda haka gaskiya gwamna ya faɗa.
"Bai kamata mutane su tsaya ana masu wani cin mutuncin ba, amma tsoro ya yi mana yawa, kowa tsoron mutuwa yake. Sai dai tambaya ɗaya zan yi wa shugabanni, shin sun sauke nauyin da ke kansu?

Dikko zai fara biyan sabon albashi

A wani rahoton kuma gwamnatin jihar Katsina ta sanar da shirin fara biyan ma'aikata mafi ƙarancin albashi na N70,000 da aka cimma matsaya da NLC.

Dikko Umaru Radda ne ya sanar da haka kuma ya ce jihar Katsina za ta kasance a gaba gaba kan maganar ƙarin albashin ma'aikata

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262