Yayin da Ambaliya ke Rusa Gidajen Kaduna, Gwamnatin Uba Sani Za Ta Gina Sabon Birni

Yayin da Ambaliya ke Rusa Gidajen Kaduna, Gwamnatin Uba Sani Za Ta Gina Sabon Birni

  • Gwamnatin Kaduna da haɗin gwiwar Urban Shelter na shirin gina sabon birni a kan fili mai girman kadada 200
  • Gwamnatin Uba Sani za ta samar da gidajen ne domin saukakawa jama'a wajen mallakar muhalli mai inganci
  • Da ya ke kaddamar da aikin, Uba Sani ya ce shirin samar da gidajen na daga cikin kokarin magance karancin muhalli

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Kaduna - Gwamnatin jihar Kaduna ta bayyana aniyarta na magance matsalar karancin muhalli da wasu mazauna jihar ke fuskanta.

Gwamna Uba Sani ne ya bayyana haka yayin kaddamar da gina gidaje a New Millennium City da gwamnati ke yi da hadin gwiwar Urban Shelter.

Kara karanta wannan

Kaduna: Ambaliyar ruwa ta lalata gidaje sama da 200, SEMA ta ɗauki mataki

Gwamna
Gwamnatin Kaduna za ta gina gidaje domin talakawa Hoto: @Abdool85
Asali: Twitter

Wannan na kunshe cikin sanarwar da babban mai ba gwamna Uba Sani shawara kan kafafen yada labarai na zamani, Abdallah Yunus Abdallah ya wallafa a shafin X.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yayin kaddamar da aikin gidajen, gwamnan wanda ya samu wakilcin matamaiyarsa, Dr. Hadiza Balarabe ya ce an yi haka ne domin saukakawa talakawa.

Za a gina gidaje 5000 a Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna ta bayyana cewa za ta gina gidaje masu sauki guda 500 a sassan jihar domin jama'a su samu gidaje masu sauki da inganci

Mataimakiyar gwamnan jihar, Dr. Hadiza Balarabe ce ta bayyana haka, inda ta ce za a gina gidaje masu sauki 5000 a fadin jihar, Jaridar Punch ta wallafa.

Kaduna: Za a gina wasu gidaje 200

Gwamnatin Uba Sani ta ce za ta gina gidaje masu sauki guda 200 a yankin Kamazou da ke karamar hukumar Chikun.

Kara karanta wannan

Dalilin da ya sa gwamnatin Sokoto ba ta biya kudin fansar Sarkin Gobir ba

Za a sayarwa jama'a gidajen a farashi mai rahusa domin sama masu muhalli mai inganci.

Gwamnati za ta gina sababbin birane

A baya kun ji cewa gwamnatin Abba Kabir Yusuf na shirin gina sabon birni a Kano, inda aka fara biyan diyyar wadanda aikin zai bi ta gonakinsu a Dawakin Kudu.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ce za a gina biranen ne domin rage cunkoso daga cikin gari, yayin da za a kara gina wasu gidajen a Unguwar Rimi da Lambu a Dawakin Kudu.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.