Yayin da Ambaliya ke Rusa Gidajen Kaduna, Gwamnatin Uba Sani Za Ta Gina Sabon Birni
- Gwamnatin Kaduna da haɗin gwiwar Urban Shelter na shirin gina sabon birni a kan fili mai girman kadada 200
- Gwamnatin Uba Sani za ta samar da gidajen ne domin saukakawa jama'a wajen mallakar muhalli mai inganci
- Da ya ke kaddamar da aikin, Uba Sani ya ce shirin samar da gidajen na daga cikin kokarin magance karancin muhalli
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Jihar Kaduna - Gwamnatin jihar Kaduna ta bayyana aniyarta na magance matsalar karancin muhalli da wasu mazauna jihar ke fuskanta.
Gwamna Uba Sani ne ya bayyana haka yayin kaddamar da gina gidaje a New Millennium City da gwamnati ke yi da hadin gwiwar Urban Shelter.

Asali: Twitter
Wannan na kunshe cikin sanarwar da babban mai ba gwamna Uba Sani shawara kan kafafen yada labarai na zamani, Abdallah Yunus Abdallah ya wallafa a shafin X.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Yayin kaddamar da aikin gidajen, gwamnan wanda ya samu wakilcin matamaiyarsa, Dr. Hadiza Balarabe ya ce an yi haka ne domin saukakawa talakawa.
Za a gina gidaje 5000 a Kaduna
Gwamnatin jihar Kaduna ta bayyana cewa za ta gina gidaje masu sauki guda 500 a sassan jihar domin jama'a su samu gidaje masu sauki da inganci
Mataimakiyar gwamnan jihar, Dr. Hadiza Balarabe ce ta bayyana haka, inda ta ce za a gina gidaje masu sauki 5000 a fadin jihar, Jaridar Punch ta wallafa.
Kaduna: Za a gina wasu gidaje 200
Gwamnatin Uba Sani ta ce za ta gina gidaje masu sauki guda 200 a yankin Kamazou da ke karamar hukumar Chikun.
Za a sayarwa jama'a gidajen a farashi mai rahusa domin sama masu muhalli mai inganci.
Gwamnati za ta gina sababbin birane
A baya kun ji cewa gwamnatin Abba Kabir Yusuf na shirin gina sabon birni a Kano, inda aka fara biyan diyyar wadanda aikin zai bi ta gonakinsu a Dawakin Kudu.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ce za a gina biranen ne domin rage cunkoso daga cikin gari, yayin da za a kara gina wasu gidajen a Unguwar Rimi da Lambu a Dawakin Kudu.
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng