Kungiyar HURIWA Ta Bukaci Tinubu Ya Yi Murabus, Ta Fadi Dalili

Kungiyar HURIWA Ta Bukaci Tinubu Ya Yi Murabus, Ta Fadi Dalili

  • Ƙungiyar marubuta masu kare haƙƙin ɗan Adam (HURIWA) ta nuna takaicinta kan yadda masu garkuwa da mutane ke cin karensu babu babbaka
  • Ƙungiyar ta buƙaci shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya murƙushe miyagun waɗanda suka addabi mutane a ƙasar nan
  • HURIWA ta kuma buƙaci Shugaba Tinubu da ya yi murabus daga kan muƙaminsa idan har ba zai iya kawo ƙarshensu ba

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Ƙungiyar marubuta masu kare haƙƙin ɗan Adam (HURIWA) ta buƙaci Shugaba Bola Tinubu da ya murƙushe masu garkuwa da mutane.

Ƙungiyar ta buƙaci shugaban ƙasan da ya yi murabus daga muƙaminsa idan har ba zai iya kawo ƙarshen miyagun ba.

Kara karanta wannan

Tsadar rayuwa: Tinubu ya sake kwantar da hankalin 'yan Najeriya, ya ba da tabbaci

An bukaci Tinubu ya yi murabus
Kungiyar HURIWA ta bukaci Tinubu ya murkushe masu garkuwa da mutane Hoto: @DOlusegun
Asali: Twitter

HURIWA ta koka kan rashin tsaro

Daily Trust ta ce a cikin wata sanarwa da jagoran ƙungiyar, Emmanuel Onwubiko, ya fitar a ranar Asabar, HURIWA ta nuna rashin jin daɗi kan matsalar rashin tsaro da ake fama da ita ta hanyar yin garkuwa da mutane da kashe-kashe a faɗin ƙasar nan.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cewar HURIWA, yanayin rashin tsaro da ake fama da shi musamman ƙaruwar kashe-kashe da sace mutane na nuna cewa Najeriya ta gaza a ƙarƙashin jagorancin Tinubu.

An buƙaci Tinubu ya yi murabus

Ƙungiyar ta ce gazawar gwamnati mai ci na magance matsalar rashin tsaro shaida ce ta gazawarta wajen magance ƙalubalen tsaro yadda ya kamata.

"Mun zo lokacin da nan ba da jimawa ba masu garkuwa da mutane za su riƙa shiga gida-gida ko su fara neman mutane su biya kuɗin kariya."

Kara karanta wannan

Kano: Binciken PCACC ya fadada yayin da aka tsare ciyamomi 3 da wasu mutum 19

"Hakan zai faru ne saboda sun tabbatar da cewa za su iya sace duk wanda suke so a kowane lokaci a duk inda yake a Najeriya."
"Idan gwamnati ba za ta iya samar da tsaro ga al'ummar ta ba, ta rasa halascinta. Saboda haka ya kamata Shugaba Tinubu ya magance matsalar rashin tsaro ko ya gaggauta yin murabus domin gwamnatinsa ta gaza wajen kare ƴan Najeriya."

- Emmanuel Onwubiko

Tinubu ya ba ƴan Najeriya haƙuri

A wani labarin kuma, kun ji cewa shugaban ƙasa Bola Tinubu ya ce duk da ƙalubalen tattalin arziƙin da ƙasar na ke fuskanta, gwamnatinsa na sane da buƙatun ƴan Najeriya.

Shugaba Bola Tinubu ya bayyana cewa gwamnatinsa ta samu nasarori sosai wajen magance wasu ƙalubalen da ƴan Najeriya ke fuskanta.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng