Kisan Sarkin Gobir: 'Yan Sanda Sun Cafke Masu Zanga Zanga, Sun Fadi Dalili

Kisan Sarkin Gobir: 'Yan Sanda Sun Cafke Masu Zanga Zanga, Sun Fadi Dalili

  • Rundunar ƴan sandan jihar Sokoto ta bayyana cewa ta cafke wasu daga cikin masu zanga-zangar nuna adawa da kisan da aka yiwa Sarkin Gobir
  • Mataikamin kakakin rundunar, Isah Mohammed a cikin wata sanarwa ya ce an cafke mutanen ne saboda ƙona dukiyoyi da kadarori a yayin zanga-zangar
  • Ya bayyana cewa ƴan sanda ba za su zura idanu su bari ɓata gari su fake da zanga-zangar ba domin tayar da rikici

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Sokoto - Rundunar ƴan sandan jihar Sokoto ta kama wasu mutane saboda zanga-zangar da aka gudanar a garin Sabon Birni.

An gudanar da zanga-zangar ne a hedkwatar ƙaramar hukumar Sabon Birni a jihar Sokoto, saboda kisan da ƴan bindiga suka yiwa Sarkin Gobir.

Kara karanta wannan

Kisan gillar sarkin Gobir: Gwamna ya dauki mataki bayan barkewar zanga zanga

'Yan sanda sun cafke masu zanga zanga a Sokoto
'Yan sanda sun kama masu zanga-zanga adawa da kisan Sarkin Gobir a Sokoto Hoto: Legit.ng
Asali: Original

Mataimakin jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, ASP Iah Mohammed ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Sokoto, cewar rahoton jaridar Vanguard.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Meyasa aka cafke masu zanga-zanga?

Ya ce wasu bata-gari a garin sun yi ƙone-ƙone ciki har da ƙona gidaje 25 da gwamnatin jihar ta gina domin zama masauki ga jami’an da aka tura domin yin aiki a yankin, rahoton Daily Post ya tabbatar.

A cewar sanarwar, rundunar za ta yi bincike sosai domin bankaɗo ƙungiyoyin da suka yi zanga-zangar a garin.

"Ƴan sanda ba za su zura idanu su bari ɓata gari su tayar da hargitsi ba da sunan zanga-zanga. Duk wanda aka samu yana da hannu a zanga-zangar zai fuskanci fushin hukuma."

- ASP Isah Mohammed

Karanta wasu labaran kan kisan Sarkin Gobir

Kara karanta wannan

Zanga zanga ta barke kan kisan Sarkin Gobir, bayanai sun fito

Matawalle ya magantu kan kisan Sarkin Gobir

A wani labarin kuma, kun ji cewa ƙaramin ministan tsaro, Bello Matawalle ya yi Allah wadai da kisan hakimin Gatawa dake ƙaramar hukumar Sabon Birni a Sakkwato wanda aka fi sani da Sarkin Gobir.

Matawalle ya bayyana kisan sarkin Gobir, Muhammad Isa Bawa a matsayin ɗanyen aiki na rashin imani, inda ya ce duk mai hannu a kisan zai ɗanɗana kuɗarsa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng