Obasanjo Ya Fayyace Gaskiya Kan Wani Sharrin da Aka Dade Ana Yi Masa

Obasanjo Ya Fayyace Gaskiya Kan Wani Sharrin da Aka Dade Ana Yi Masa

  • An daɗe ana cece-kuce game da batun cewa tatson tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo ya fito daga ƙabilar Igbo
  • Wasu dai sun yi iƙirarin cewa mahaifin tsohon shugaban ƙasar haifaffen ƙabilar Igbo ne daga jihar Anambra a yankin Kudu maso Gabashin Najeriya
  • A karon farko Obasanjo ya mayar da martani inda ya bayyana iƙirarin a matsayin abin dariya sannan ya buƙaci ƴan Najeriya su haɗa kawunansu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Ogun - A karon farko tsohon shugaban ƙasa Cif Olusegun Obasanjo ya musanta shi ɗan ƙabilar Igbo ne, inda ya bayyana cewa lamarin yana ba shi dariya

Obasanjo ya ƙara da cewa, Najeriya ta dukkanin ƴan Najeriya ce ba tare da la’akari da bambancin al’adu ba.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun kai hari ana tsakiyar shagalin biki, sun tafka mummunar ɓarna

Obasanjo ya musanta shi Igbo ne
Obasanjo ya musanta cewa asalinsa kabilar Igbo ne Hoto: Olusegun Obasanjo
Asali: Facebook

Wasu dai sun daɗe suna zargin cewa mahaifin Obasanjo ya fito ne daga jihar Anambra.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa a lokacin da ake tunkarar zaɓen 2023, an zargi tsohon shugaban ƙasar da marawa Peter Obi na jam’iyyar Labour Party baya, saboda tatsonsa na Igbo.

Wane martani Obasanjo ya yi?

A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Kehinde Akinyemi, ya fitar a ranar Juma’a, 16 ga watan Agusta, Obasanjo ya yi tsokaci kan batun tsatsonsa na ƙabilar Igbo ne.

"Lamarin yana ba ni dariya."

- Olusegun Obasanjo

Jaridar The Punch ta ruwaito cewa Obasanjo ya yi wannan jawabi ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin shugabannin ƙungiyar kasuwa ta Ndigbo Amaka a birnin Abeokuta na jihar Ogun.

Karanta wasu labaran kan Obasanjo

Kara karanta wannan

Bayan fadin albashin sanatoci, Kawu Sumaila ya yi sabuwar fallasa

Obasanjo ya fallasa ƴan majalisu

A wani labarin kuma, kun ji cewa tohon shugaban ƙasa Cif Olusegun Obasanjo ya zargi ƴan majalisar dattawa da ta wakilai da ƙayyade albashinsu da kansu.

A cewar tsohon shugaban ƙasan, ƴan majalisar tarayya sun samu Naira miliyan 200 kowannensu, kuma sun sanya hannu sun karɓa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng