Farfesa Ya Hango Abin da Zai Tayar da Hankalin Tinubu, Ya Yi Gargadi

Farfesa Ya Hango Abin da Zai Tayar da Hankalin Tinubu, Ya Yi Gargadi

  • Farfesa Toyin Falola na jam'iar Texas ya yi magana kan zanga-zangar nuna adawa da halin ƙuncin da aka yi a ƙasar nan
  • Farfesan ya bayyana cewa Shugaba Bola Tinubu bai magance matsalolin da suka sanya mutane suka fito kan tituna
  • Ya gargaɗi shugaban ƙasan kan ya ji tsoron aukuwar irin zanga-zangar da aka yi a ƙasar Bangladesh wacce ta sanya Firaministar ƙasar ta gudu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Legas - Shahararren farfesan tarihi, Toyin Falola, ya ce gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta gaza magance manyan matsalolin da suka haddasa zanga-zangar #EndBadBadGovernance.

Farfesan ya bayyana cewa Tinubu bai yi magana kan hanyoyin magance yunwa, tsadar rayuwa da rashin tsaro waɗanda su ne suka haifar da zanga-zangar ba.

Kara karanta wannan

An kama wasu ƴan siyasa da suka ba masu zanga zanga N4bn a Abuja da jihohin Arewa 3

Farfesa ya ba Tinubu shawara
Farfesa Toyin Falola ya gargadi Shugaba Bola Tinubu @DOlusegun
Asali: Facebook

Farfesa Toyin Falola na jami'ar Texas ya bayyana hakan ne a cikin shirin 'Inside Sources' na tashar Channels tv a ranar Juma'a.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ce masu zanga-zangar sun kyauta wajen sanar da zanga-zangar makonni kafin farawa domin ba gwamnati lokaci ta tsara dabarun magance rikicin da za a iya samu.

Wacce shawara farfesan ya ba Tinubu?

Farfesa Toyin Falola, ya ce kamata ya yi gwamnatin Tinubu ta ji tsoron zanga-zangar da ba za a iya shawo kanta ba kamar yadda aka yi a ƙasar Bangladesh.

"Lokacin da shugaban ƙasa ya yi jawabinsa, babu magana a kan tallafin man fetur, ababen more rayuwa, wutar lantarki da tsaro, waɗanda su ne suka sanya aka yi zanga-zangar.
"Martanin da ke fitowa daga fadar Aso Rock kawai shi ne 'ba mu son wani ya kawo cikas ga gwamnati.' Babu wanda yake son ya hargitsa gwamnati."

Kara karanta wannan

Katsina: Gwamna ya sauya dokar da ya sanya lokacin zanga zanga a Najeriya

- Farfesa Toyin Falola

"Tinubu ya san akwai yunwa", Toyin

Ya bayyana babu yadda za a yi a ce Tinubu bai san yadda rayuwa ta yi tsada ba a Najeriya.

"Tinubu ya san halin da ake ciki, sannan ci gaba da neman uzuri ba shi ba ne hanyar gudanar da mulki. Amma daga ƙarshe mun yi sa'a ba a yi ɓarna ba. Mutane sun yi tsammanin faɗan Yarbawa da Igbo a Legas amma ba a yi ba."
"Abubuwan da suka sanya aka yi zanga-zangar ba a magance su ba. Abin da ya kamata gwamnati ta mayar da hankali a kai shi ne zanga-zanga wacce ba a shirya ba kuma ba a sanar ba, wannan ta fi hatsari."
"Saboda wannan ba za a iya yin komai a kanta ba. Wannan wacce aka yi an sanar wanda ya ba da dama aka samar da jami'an tsaro a kan hanya. Amma zanga-zangar da za a ji tsoro, ita ce irin ta Bangaladesh."

Kara karanta wannan

Jerin muhimman abubuwa 3 da Tinubu ya ƙara masu kudi daga hawa mulki zuwa yau

- Farfesa Toyin Falola

Karanta wasu labaran kan Tinubu

Halin da Tinubu ya gaji tattalin arziƙi

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta bayyana cewa ta gaji tattalin arzikin ƙasa a cikin mawuyacin hali daga tsohon shugaba, Muhammadu Buhari.

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya fadi haka ne yayin kaddamar da littafi mai suna 'gano siyasar tsare-tsaren ilimin bai daya na Najeriya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng