Dan Bello Ya Sake Kwancewa Gwamnatin Tinubu Zani a Kasuwa

Dan Bello Ya Sake Kwancewa Gwamnatin Tinubu Zani a Kasuwa

  • Bello Habib Galadanci wanda aka fi sani da Dan Bello ya fito ya ƙara yi wa shugaba Bola Tinubu wankin babban bargo
  • Dan Bello ya bayyana cewa ƴan Najeriya na fama da yunwa saboda tsare-tsaren da gwamnati mai ci ta kawo
  • Ya ƙalubalanci gwamnati da ta shigar da shi ƙara a kotu idan har ba ta jin daɗin wayar da kan jama'an da yake yi

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Bello Habib Galadanchi, wanda aka fi sani da Dan Bello, ya sake caccakar gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.

Dan Bello ya bayyana cewa yunwa na kashe ƴan Najeriya saboda manufofin Shugaba Bola Tinubu.

Dan Bello ya caccaki gwamnatin Tinubu
Dan Bello ya caccaki manufofin gwamnatin Bola Tinubu Hoto: Aliyu Jalal, Olusegun Dada
Asali: Facebook

Dan Bello ya ƙalubalanci gwamnati

Kara karanta wannan

Gwamnatin tarayya ta fadi hanyar da za a iya raba Tinubu da mulkin Najeriya

Dan Bello ya bayyana hakan ne a wata hira da yayi da gidan talabijin na Trust tv a ranar Talata.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ƙalubalanci gwamnati da ta shigar da ƙara a kansa idan har ba ta jin daɗin yadda yake ƙware mata zani a kasuwa.

Dan Bello ya ce ba ya da alaƙa da wata jam’iyyar siyasa a ƙasar, yana mai cewa babu wanda yake yiwa aiki, rahoton Daily Trust ya tabbatar.

Me Dan Bello ya ce kan gwamnatin Tinubu?

"Idan har abin da na ke yi bai yi musu daɗi ba, hakan na nufin jama'a na jin daɗinsa. Idan abin da suke yi mai kyau ne babu wanda zai ji cewa bidiyoyin da na ke yi suna taka wata rawa."
"Hakan na nufin cewa ba su yin ƙoƙarin da ya dace. Abin da suke yi duk shi ya jawo wannan matsalolin da muke fuskanta."

Kara karanta wannan

"Yana da kyakkyawan shiri": Hadimin Tinubu ya kwantar da hankalin matasan Najeriya

"Jam'iyya mai mulki ta kawo tsare-tsare da suka jefa mutane cikin yunwa. Mutane na mutuwa. Mutane yanzu na cin ciyawa. Mutane na shan gurɓataccen ruwa. Mutane na zuwa suna cewa ba su ci abinci ba na tsawon kwana uku."
"Wannan ba annoba ba ce ta ruwan sama ko iska mai ƙarfi. Hakan ya auku ne saboda wasu tsare-tsare waɗanda za a iya kauce musu. Waɗannan shugabannin kawai sun kawo tsare-tsare sannan sun toshe kunnuwansu."
"Yanzu ba su jin daɗi saboda suna samun biliyoyin kuɗi ta hanyar yin gurɓatattun ayyuka. Eh ina son su ƙi jin daɗin, ina son su je kotu. Ina son su shigar da ƙara, su yi duk abin da za su iya domin mu yi shiru. Hakan ya nuna cewa aikinmu na yin kyau."

- Bello Habib Galadanci

Yaron El-Rufai ya ba Dan Bello shawara

A wani labarin kuma, kun ji cewa Bashir Nasir El-Rufai ya yi kira ga Bello Habib Galadanci wanda aka fi sani da Dan Bello kan bidiyoyin da yake yi.

Kara karanta wannan

"Ka kore su": Jigon APC ya ba Tinubu lakanin gyara Najeriya

Yaron na tsohon gwamnan jihar Kaduna ya faɗawa Bello Habib Galadanci ya yi hattara da yadda yake fitar da bidiyoyi da ƙoƙarin faɗakar da al’umma.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng