"Yana da Kyakkyawan Shiri": Hadimin Tinubu Ya Kwantar da Hankalin Matasan Najeriya

"Yana da Kyakkyawan Shiri": Hadimin Tinubu Ya Kwantar da Hankalin Matasan Najeriya

  • Babban mataimaki na musamman ga shugaba Bola Ahmed Tinubu kan harkokin ɗalibai ya buƙaci matasa da su ƙara kai zuciya nesa
  • Asefon Sunday ya buƙaci matasan Najeriya da su ƙara haƙuri da gwamnatin Tinubu domin yana da kyakkyawan shiri a kansu
  • Hadimin na shugaban ƙasan ya buƙaci matasan da kada su bari wasu maƙiyan ƙasar nan su yi amfani da su domin cimma wata buƙata

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Benue - Babban mataimaki na musamman ga shugaban ƙasa kan harkokin ɗalibai, Asefon Sunday, ya tunatar da matasa shirin Shugaba Bola Tinubu a kansu

Hadimin na Shugaba Tinubu ya yi kira ga matasan Najeriya da su ƙara haƙuri da wannan gwamnati mai ci.

Kara karanta wannan

"Ka kore su": Jigon APC ya ba Tinubu lakanin gyara Najeriya

An fadi shirin Tinubu kan matasa
Hadimin Tinubu ya ba matasan Najeriya hakuri Hoto: @DOlusegun
Asali: Facebook

Hadimin Bola Tinubu ya roƙi matasan Najeriya

Asefon Sunday ya yi wannan roƙo ne a garin Makurdi a lokacin da yake zantawa da manema labarai, cewar rahoton jaridar The Punch.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya zanta da maneman labaran ne yayin wani shirin horar da wasu shugabannin ƙungiyoyin ɗalibai na manyan makarantu na tsawon kwanaki uku.

Shirin ba da horon, mai taken, ‘Gina shugabannin matasa masu kishin ci gaban ƙasa’, ya samu mahalarta daga yankin Arewa ta tsakiya.

Shirin gwamnatin Tinubu kan matasa

Ya bayyana cewa gwamnatin Tinubu tana da kyakkyawan shiri kan matasa sannan ya buƙace su da kada su bari a yi amfani wajen kawo hargitsi a ƙasar nan, rahoton jaridar Tribune ya tabbatar.

"Ina kira ga matasa da su ƙara haƙuri da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu saboda yana da kyakkyawan shiri a kansu."

Kara karanta wannan

Atiku ya caccaki Tinubu, ya bayyana inda gwamnatinsa ta samu matsala

"Ka da su bari maƙiyan ƙasar nan su yi amfani da su saboda akwai mutane da dama waɗanda tsare-tsaren wannan gwamnatin ba su yi daidai da ra'ayinsu ba.
"Waɗanda suka kwashe arziƙin ƙasar nan su ne suke son yin amfani da matasa da ɗalibai domin yin zanga-zangar da za ta kawo cikas ga gwamnati."

- Asefon Sunday

Karanta wasu labaran kan Tinubu

Jigon APC ya ba Tinubu shawara

A wani labarin kuma, kun ji cewa wani jigo a jam’iyyar APC, Jesutega Onokpasa, ya ba shugaban ƙasa Bola Tinubu, shawara kan hanyar gyara Najeriya.

Jesutega ya shawarci Tinubu da ya samar da ƙwararrun ƴan Najeriya a kusa da shi domin ya samu damar gyara kura-kuran da gwamnatocin baya suka yi da kuma cimma tsare-tsarensa kan tattalin arziƙin Najeriya.

Kara karanta wannan

Olusegun Obasanjo ya fadi hanyar da Najeriya za ta samu ci gaba

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng