Tsohon Sanata Ya Fadi Manufar Rikicin da Aka Samu Sakamakon Zanga Zanga

Tsohon Sanata Ya Fadi Manufar Rikicin da Aka Samu Sakamakon Zanga Zanga

  • Tsohon sanatan Kaduna ta Tsakiya ya yi Allah wadai da barnar da aka samu a sakamakon zanga-zanga da ake yi a faɗin ƙasar nan
  • Sanata Shehu Sani ya bayyana cewa rikicen-rikicen da aka samu a Arewacin Najeriya wani yunƙuri ne na kifar da gwamnati
  • Ya yi zargin cewa an rabawa matasa kuɗaɗe da tutocin Rasha yayin zanga-zangar wacce ake yi domin nuna adawa da halin ƙuncin

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Tsohon sanatan Kaduna ta Tsakiya, Shehu Sani, ya yi magana kan rikice-rikicen da aka samu sakamakon zanga-zangar da ake yi a faɗin ƙasar nan.

Sanata Shehu Sani, ya yi Allah-wadai da tashe-tashen hankulan da aka samu a Arewacin Najeriya sakamakon zanga-zangar.

Kara karanta wannan

Kasar Rasha ta yi magana kan masu zanga zangar da ke ɗaga tutocinta a Najeriya

Shehu Sani ya yi magana kan zanga-zanga
Shehu Sani ya yi Allah wadai da rikicin da aka samu sakamakon zanga-zanga Hoto: Shehu Sani
Asali: Facebook

Wane zargi Shehu Sani ya yi?

Shehu Sani wanda aka yi hira da shi a tashar Channels tv ranar Talata, ya ce tashe-tashen hankulan wani yunƙuri ne na kifar da gwamnati.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya yi zargin cewa kwana ɗaya kafin zanga-zangar an raba kuɗaɗe da tutocin ƙasashen waje a tsakanin matasa.

"Kwana ɗaya kafin zanga-zangar ƙarshe, an raba kuɗi ga matasa da tutocin ƙasar Rasha. Hakan ya nuna cewa gabaɗaya manufar zanga-zangar ba domin tsare-tsaren gwamnati ba ne."
"An yi yunƙurin samar da wani yanayi ne wanda za a kifar da gwamnati. Idan aka samu irin haka, za ka ga cewa akwai wanda ke kitsa yadda za a samu karya doka da oda."

- Shehu Sani

An yi rikici yayin zanga-zanga a Arewa

A yayin zanga-zangar da aka yi a Kaduna, Kano da wasu jihohin Arewacin Najeriya, wasu matasa sun riƙa ɗaga tutocin Rasha yayin da suke kiran sojoji da su amshi mulki.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: An kama mutumin da ke ɗinka tutocin ƙasar Rasha a jihar Kano

An fara zanga-zangar #EndBadGovernance ne a ranar, 1 ga watan Agusta kuma ana sa ran za a ɗauki tsawon kwanaki 10 ana yi.

Karanta wasu labaran kan zanga-zanga

Shehu Sani ya magantu kan zanga-zanga

A wani labarin kuma, kun ji cewa tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya a majalisar dattawa ta takwas, Shehu Sani, ya yi magana kan abubuwan da ke sanyawa zanga-zangar lumana ta rikiɗe ta koma tashin hankali.

Shehu Sani ya bayyana cewa idan jami'an tsaro ɗauke da makamai suka harbi masu zanga-zanaga, tana iya rikiɗewa ta koma tashin hankali.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng