Zanga Zanga: 'Yan Sanda Sun Jaddada Dokar Hana Fita a Katsina

Zanga Zanga: 'Yan Sanda Sun Jaddada Dokar Hana Fita a Katsina

  • Rundunar 'yan sandan jihar Katsina ta jaddada dokar hana zirga-zirga inda ta ja kunnen wadanda ke shirin fita zanga-zanga
  • A wasu wuraren da ke jihar, an sanya dokar hana fita na awanni 24, inda a wasu wuraren aka sanya ta awa 12
  • Haka kuma an haramta taro a dukkanin sassan jihar yayin da zanga-zangar ta shiga rana ta biyar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Katsina - Rundunar 'yan sandan Katsina ta jaddada dokar hana zirga-zirga a fadin jihar yayin da zanga-zanga ta shiga rana ta biyar.

An fara gudanar da zanga-zanga a ranar Alhamis 1 Agusta, 2024 domin nuna adawa da manufofin shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu.

Kara karanta wannan

Dokar takaita fita: Jami'ar BUK ta dauki matakin kare dalibai a Kano

Police
Yan sanda sun ja kunnen masu zanga-zanga Hoto: Nigeria Police Force
Asali: Facebook

Jaridar The Sun ta wallafa cewa jami'in hulda da jama'a na rundunar yan sandan Katsina, ASP Abubakar Sadiq ne ya jaddada dokar hana fita.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Za mu kama masu zanga-zanga," Yan Sanda

Rundunar yan sandan Katsina ta ce duk wanda aka kama da saɓa dokar hana fita da sunan zanga-zanga a jihar zai fuskanci fushin hukuma, Punch ta wallafa.

Da ya ke tabbatarwa Legit da ci gaba da hana fitar, ASP Abubakar Sadiq ya ce an sanya 7.00pm-7.00a.m - awanni 12 ke nan a matsayin lokacin da aka hana yawo.

Ya ce ba za su amince a rika karya dokar gwamnati na kokarin tabbatar da wanzuwar zaman lafiya a sassan jihar ba yayin zanga-zanga.

An kafa dokar hana yawo a Katsina

A baya mukaddashin gwamnan jihar Katsina, Faruq Jobe ya sanya dokar hana fita a karamar hukumar Dutsinma.

Kara karanta wannan

Matsin rayuwa: Bayan rasa rayuka, masu zanga zanga sun fara alkunutu a Kano

Haka kuma ya ce gwamnati ba za ta lamunci gudanar da kowane irin taro a kokarin samar da zaman lafiya.

'Yan sanda sun kama mai zanga zanga

A wani labarin kun ji cewa jami'an 'yan sandan Kano sun cafke matashin da ya ke raba tutar kasar Rasha ga matasa su na dagawa a fadin jihar.

A yau da aka shiga rana ta biyar na zanga-zanga a fadin Najeriya, an gano matasa su na daga tutar kasar Rasha su na neman taimakon Vladimir Putin.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.