Shugaba Tinubu Ya Fadi Abu 1 da ba Zai Lamunta ba a Najeriya

Shugaba Tinubu Ya Fadi Abu 1 da ba Zai Lamunta ba a Najeriya

  • Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana irin Najeriyar da yake son ginawa a lokacin mulkinsa
  • Shugaba Tinubu ya bayyana cewa ko kaɗan ba zai lamunci ayyukan masu nuna bambancin ƙabilanci ba a ƙasar nan
  • Shugaban ƙasan ya ja kunnensu tare da yin gargaɗin cewa doka za ta yi aiki a kan duk wani mai yiwa wata ƙabila barazana a ƙasar nan

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce Najeriyar da yake son ginawa ba ta da wurin nuna bambancin ƙabilanci.

Shugaba Tinubu ya bayyana haka ne a safiyar Lahadi a Abuja yayin da yake jawabi kan zanga-zangar #Endbadgovernance da ake yi a faɗin ƙasar nan.

Kara karanta wannan

Ana jira ya dawo da tallafi, Tinubu ya aika da sako mai zafi ga masu zanga zanga

Tinubu ya yi gargadi
Shugaba Tinubu ya gargadi masu nuna bambancin kabilanci Hoto: @DOlusegun
Asali: Twitter

Ya gargaɗi ɓata garin da suka yiwa sauran ƙabilun ƙasar nan barazana da su daina, yana mai cewa doka za ta yi aiki a kansu, cewar rahoton jaridar The Punch.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Zanga-zanga ta bar baya da ƙura

Zanga-zangar kwanaki 10 da aka shirya, wacce aka fara ranar Alhamis, musamman domin nuna adawa da tsadar rayuwa da yunwa, ta rikiɗe zuwa tashe-tashen hankula, ɓarnata dukiya da asarar rayuka a sassa da dama na ƙasar nan.

Wasu ɓata gari a kafafen sada zumunta sun buƙaci ƴan ƙabilar Igbo da su fice daga Legas ko su fuskanci zanga-zangar da aka shirya a tsakanin ranakun 20 zuwa 30 ga watan Agustan 2024, cewar rahoton Sahara Reporters.

Masu yin rubuce-rubucen sun kuma umarci ƴan yankin Kudu maso Yamma da ke zaune a yankin Kudu maso Gabas da su dawo gida kafin fara zanga-zangar.⁣

Kara karanta wannan

Babban lauya ya ba Tinubu lakanin kawo karshen zanga zangar da ake yi

Wane gargaɗi Shugaba Tinubu ya yi

Ana cikin hakan, Shugaba Tinubu ya yi martani kan masu yin waɗannan kiraye-kirayen.

"Ga waɗanda suke amfani da wannan damar domin yin barazana ga wani yanki a ƙasar nan, ku shiga taitayinku."
"Doka za ta yi aiki a kanku. Babu wurin nuna bambancin ƙabilanci ko irin wannan barazanar a Najeriyar da muke son ginawa."
"Dimokuraɗiyyarmu za ta ci gaba ne lokacin da aka kare tare da mutunta ƴancin kowane ɗan Najeriya."

- Bola Tinubu

Tinubu ya shawarci masu zanga-zanga

A wani labarin kuma, kun ji cewa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci masu zanga-zangar adawa da gwamnatinsa da su dakatar da ita.

Shugaban ƙasan ya yi kira a gare su da su haƙura su zo a tattauna domin samun mafita kan hanyoyin da za a magance matsalolin da suke kuka da su.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng