Zanga Zanga: Daga Karshe Tinubu Ya Sanya Lokacin Yin Jawabi ga 'Yan Najeriya

Zanga Zanga: Daga Karshe Tinubu Ya Sanya Lokacin Yin Jawabi ga 'Yan Najeriya

  • Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai yi jawabi ga ƴan Najeriya yayin da ake ci gaba da zanga-zanga a faɗin ƙasar nan
  • Shugaba Tinubu zai yi jawabin ne na kai tsaye ga ƴan al'ummar Najeriya da ƙarfe 7:00 na safiyar ranar Lahadi, 4 ga watan Agustan 2024
  • Dubunnan matasa ne dai suka fito kan tituna domin nuna adawa da halin matsin tattalin arziƙi da yunwar da ake fama da ita a ƙasar nan

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai yi jawabin kai tsaye ga ƴan Najeriya a ranar Lahadi, 4 ga watan Agustan 2024.

Shugaban ƙasan zai gudanar da jawabin ne da misalin ƙarfe 7:00 na safiyar ranar Lahadi.

Kara karanta wannan

Babban lauya ya ba Tinubu lakanin kawo karshen zanga zangar da ake yi

Tinubu zai yiwa 'yan Najeriya jawabi
Tinubu zai yi jawabi ga 'yan Najeriya ranar Lahadi Hoto: @DOlusegun
Asali: Twitter

Tinubu zai yi jawabi ga ƴan Najeriya

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar, Ajuri Ngelale, ya fitar da yammacin ranar Asabar, 3 ga watan Agustan 2024, a shafinsa na Facebook.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Shugaban ƙasa Bola Tinubu zai yi jawabi ga al'ummar Najeriya a ranar Lahadi, 4 ga watan Agusta, 2024 da misalin ƙarfe 7:00 na safe."
"Gidajen talbijin, rediyo da sauran kafafen watsa labarai su kama tashar NTA da gidan rediyon Najeriya (FRCN) domin jawabin."
"Za a maimaita jawabin a tashoshin NTA da FRCN da ƙarfe 3:00 na yamma da ƙarfe 7:00 na yamma a ranar Lahadi."

- Ajuri Ngelale

Karanta wasu labaran kan zanga-zanga

Kara karanta wannan

Duk da katobarar da ya yi, Akpabio ya sake neman wata bukata wajen 'yan Najeriya

Uba Sani ya caccaki jagororin zanga-zanga

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, ya caccaki masu shirya zanga-zangar #EndBadGovernance a jihar bisa zargin ƙin fitowa su jagoranci zanga-zangar.

A cewar Uba Sani, maimakon su jagoranci zanga-zangar, sai suka fake suka bar matasa marasa galihu su jagoranci zanga-zangar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng