Gwamna Ya Fito Ya Fadi Babban Kuskuren Masu Shirya Zanga Zanga

Gwamna Ya Fito Ya Fadi Babban Kuskuren Masu Shirya Zanga Zanga

  • Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, ya fito ya nuna takaicinsa kan rashin fitowar da masu shirya zanga-zanga suka yi a jihar
  • Gwamnan ya nuna rashin fitowa su jagoranci zanga-zangar kuskure ne domin hakan ya jawo wasu ɓata gari sun yi amfani da ita wajen yin sata
  • Ya nuna cewa su a baya da suka jagoranci zanga-zanga, ba su bari an kama wasu ba, su kawai aka kama

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Kaduna - Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, ya caccaki masu shirya zanga-zangar #EndBadGovernance a jihar bisa zargin ƙin fitowa su jagoranci zanga-zangar.

A cewar Uba Sani, maimakon su jagoranci zanga-zangar, sai suka fake suka bar matasa marasa galihu su jagoranci zanga-zangar.

Kara karanta wannan

Sarki Muhammadu Sanusi II ya fadi abin da za ayi da kayan 'ganimar' zanga-zanga

Uba Sani ya soki masu shirya zanga-zanga a Kaduna
Gwamna Uba Sani bai ji dadin satar da aka yi ba yayin zanga-zanga a Kaduna Hoto: Senator Uba Sani
Asali: Facebook

Gwamnan, ya bayyana hakan yayin wata hira da ya yi da gidan jaridar BBC Hausa a ranar Asabar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Me Uba Sani ya ce kan zanga-zanga?

Gwamna Uba Sani ya ce idan masu shirya zanga-zangar na kusa da sun gargaɗi matasan da suka yi amfani da zanga-zangar wajen yin sata.

"Mu a baya da muka fito muka jagoranci zanga-zanga an kama mu. Ba mu taɓa bari a kama matasa da sauran jama’a da suka fito zanga-zanga tare da mu ba. Mu ne aka kama."
"Idan kuna kiran a fito zanga-zanga, ku ne ya kamata ku yi kan gaba wajen fitowa. Suna ta magana a shafukan sada zumunta, amma ba su fito a lokacin zanga-zangar ba."
"Da a ce suna nan, da za ta fi kyau domin aƙalla, da sun gargaɗi matasan da ke fasa shagunan jama’a da wawashe dukiyar jama’a, amma ba su fito ba, ƴaƴansu ba su fito ba. Ƴaƴan talakawa ne suka fito yayin zanga-zangar. Ina ganin hakan bai dace ba."

Kara karanta wannan

Gwamna ya zargi wasu manyan ƴan siyasa da hannu a rura wutar zanga zanga

- Uba Sani

Gwamna Uba Sani ya zargi ƴan adawa

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, ya yi zargin cewa ƴan adawa na amfani da zanga-zangar da ake yi domin ɗaukar fansar kashin da suka sha a zaɓen 2023.

Gwamnan ya yi iƙirarin cewa wasu ƴan adawa ne ke tunzura matasa da sauran talakawa su shiga zanga-zangar da aka fara ranar Alhamis, 1 ga watan Agusta.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng