Kungiyar NLC Ta Dakatar da Zanga Zanga? Gaskiya Ta Bayyana

Kungiyar NLC Ta Dakatar da Zanga Zanga? Gaskiya Ta Bayyana

  • Ƙungiyar NLC ta sake nanata cewa ba ita ce ta shirya zanga-zangar adawa da halin ƙuncin da ake fama da shi wacce ake gudanarwa a faɗin ƙasar nan
  • NLC ta fitar da wata sanarwa inda ta musanta cewa ba ta dakatar da zanga-zangar da ake gudanarwa ba a faɗin ƙasar nan
  • Dubunnan mutane ne suka fito kan tituna a biranen Najeriya a zanga-zangar nuna adawa da taɓarɓarewar tattalin arziƙi da wahalar da ake sha

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa (NLC) ta yi watsi da rahotannin da ke cewa ta dakatar da zanga-zangar nuna adawa da halin ƙuncin da ake ciki a ƙasar nan.

Ƙungiyar NLC ta kuma musanta cewa ta sake matsayarta kan zanga-zangar wacce ake yi a faɗin ƙasar nan.

Kara karanta wannan

Masu zanga zanga sun dira gidan Buhari a Daura, bayanai sun fito daga Katsina

NLC ta musanta dakatar da zanga-zanga
Kungiyar NLC ta musanta dakatar da zanga-zanga Hoto: @NLCHeadquarters
Asali: Twitter

A wata sanarwa da ta fitar a yammacin ranar Juma’a, 2 ga watan Agusta a shafinta na X, ƙungiyar ta NLC ta musanta rahotannin cewa ta dakatar da zanga-zangar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Matsayar NLC kan zanga-zanga

A watan Yuli ne ƙungiyar NLC ta bayyana cewa ba ita ce ta shirya zanga-zangar adawa da halin ƙunci a faɗin ƙasar nan ba.

A lokacin, ƙungiyar ta mayar da martani ga rahotannin da ke cewa ta janye daga shiga zanga-zangar ta ƙasa.

A ranar Juma’a, 2 ga Agusta, 2024, rahotanni daban-daban guda biyu sun bayyana.

Wani rahoton ya yi iƙirarin cewa ƙungiyar kwadago ta sanar da dakatar da zanga-zangar, yayin da wani kuma ya ce NLC ta sake duba matsayarta kan zanga-zangar.

Wane martani NLC ta yi?

Yanzu dai ƙungiyar NLC ta mayar da martani a hukumance kan wannan jita-jita.

Kara karanta wannan

Zanga zangar adawa da Tinubu ta samu gagarumar matsala awanni kafin a fara

NLC ta bayyana cewa jita-jitar da ake yaɗawa maganar da ta yi ne a lokacin da aka fara shirin zanga-zanga, inda ta ba gwamnati shawara domin ta tattauna da masu shirya ta.

Ta bayyana cewa har yanzu tana kan wannan matsayar na ganin gwamnati ta tattauna da masu zanga-zangar domin hakan shi ne mafita.

Lauya ya ba Tinubu shawara

A wani labarin kuma, kun ji cewa lauyan kare haƙƙiin ɗan Adam, Inibehe Effiong, ya bayyana abin da ya kamata Shugaba Bola Tinubu ya yi domin shawo kan matasa masu zanga-zanga.

Dubunnan ƴan Najeriya da suka fusata ne suka fito manyan biranen ƙasar nan domin gudanar da zanga-zangar nuna adawa da halin ƙuncin da ake ciki.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng