Rana ta 3: Gwiwar Masu Zanga Zanga Ta Fara Sanyi, Jama'a Ba Su Fito a Abuja ba

Rana ta 3: Gwiwar Masu Zanga Zanga Ta Fara Sanyi, Jama'a Ba Su Fito a Abuja ba

  • A yau Asabar ne aka shiga rana ta uku daga cikin kwanaki 10 da za a gudanar da zanga-zanga a Najeriya
  • 'Yan kasar nan sun fusata biyo bayan matsin rayuwa da su ke ganin manufofin shugaba Bola Tinubu ne ya jawo
  • Sai dai a yau, jama'a ba su fito sosai a babban birnin tarayya Abuja ba inda ake sa ran ci gaba da zanga zanga domin tura sako ga shugaba Tinubu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

FCT, Abuja - Gwiwar jama'a ta fara sanyi yayin da aka samu karancin masu ci gaba da zanga-zanga a rana ta uku a baban birnin tarayya Abuja.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: 'Yan sandan Kano sun tashi tsaye, an fara bin gida gida neman kayan sata

Kwanaki 10 cir 'yan kasar nan su ka bayyana cewa za su yi su na zanga-zangar lumana ta nuna rashin jin dadin manufofin shugaba Bola Tinubu.

Protest
Masu zanga-zanga sun yi zamansu a gida a rana ta 3 Hoto: Reno Omokri
Asali: Facebook

A labarin da ya kebanta da Daily Trust, an tabbatar da cewa mutane ba su yi fitowar da aka yi a kwanaki biyun farko na zanga-zanga ba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ko mutum 1 babu da sunan zanga-zanga

Ko mutum daya ba a gani a filin wasan Abuja a ranar Asabar ba yayin da jami'an tsaro ke ci gaba da rangadi tun da har yanzu ana cikin kwanaki 10 zanga-zanga.

An gano 'yan sanda da 'yan jarida sun yi cirko-cirko su na jiran abin da zai faru domin akwai yiwuwar a fito ci gaba da zanga-zangar.

"Masu zanga-zanga na hutu," dan sanda

Daga cikin jami'an tsaron da ke tsaye su na kokarin tabbatar da tsaro a filin wasan Abuja ya yi shagube ga masu zanga-zanga.

Kara karanta wannan

Sanata mai ci na daukar nauyin masu zanga zanga? gaskiya ta fito

Da ya juya ya kalli abokin aikinsa, dan sandan ya ce su masu zanga-zanga sun tafi hutun karshen mako.

Masu zanga-zanga sun fito a Jigawa

A wani labarin kun ji yadda jama'a a Jigawa su ka yi watsi da umarnin gwamnatin jihar na cewa kowa ya zauna a gida, inda su ka fito zanga-zanga.

Tun a rana ta farko aka samu wasu fusatattun matasa su ka kona ofishin jam'iyyar APC a jihar, inda aka samu rahotannin 'yan daba sun shiga lamarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.