Rana Ta 2: Ƴan Sanda Sun Bude Wa Masu Zanga Zanga Wuta, Mutane da Yasa Sun Jikkata

Rana Ta 2: Ƴan Sanda Sun Bude Wa Masu Zanga Zanga Wuta, Mutane da Yasa Sun Jikkata

  • Masu zanga-zanga sun gamu da fushin ƴan sanda yayin da suka sake taruwa a kusa da babban asibitin ƙasa a birnin Abuja yau Jumu'a
  • Matasan sun sake taruwa duk da kashedin da rundunar ƴan sanda ta yi bayan tayar da hargitsi a rana ta farko da suka fara zanga-zanga
  • Ana fargabar mutum biyar sun jikkata lokacin da yan sandan suka yi harbe-harbe da fesa hayaki mai sa hawaye don tarwatsa matasan

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Ana fargabar masu zanga-zanga da dama sun samu raunuka yayin da ƴan sanda suka tarwatsa su a babban birnin tarayya Abuja yau Jumu'a.

Tun da safe dai masu zanga-zangar suka sake fitowa a rana ta biyu, inda suka taru a bayan babban asibitin ƙasa da ke Abuja duk da kashedin rundunar ƴan sanda.

Kara karanta wannan

Rana Ta 2: Rundunar Sojoji ta shirya ɗaukar mataki mai tsauri kan masu zanga zanga

Masu zanga zanga.
Ana fargabar mutane sun jikkata yayin da ‘yan sanda suka tarwatsa masu zanga-zanga a Abuja Hoto: Contributor
Asali: Facebook

Ƴan sanda sun yi kashedi kan zanga-zanga

Kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito, tun farko rundunar ƴan sandan Abuja ta gargaɗi masu zanga-zangar cewa kar su fito saboda abubuwan da suka faru a ranar farko.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sai dai masu zanga-zangar sun yi fatali da kashedin ƴan sanda, inda suka sake taruwa a kusa da babban asibiti na ƙasa yau Jumu'a, a rahoton The Cable.

Jami’an ‘yan sandan sun mamayi masu zanga-zangar a bayan Asibitin kasa, suka tarwatsa su da barkonon tsohuwa da harsasai masu rai.

Yadda ƴan sanda suka buɗe wuta

Da suke magana da manema labarai, wasu mutum biyar daga cikin masu zanga-zangar waɗanda suka samu raunuka sun soki ‘yan sanda kan abin da suka aikata.

Sun yi ikirarin cewa sai da suka yi tsalle suka faɗa cikin daji lokacin da ‘yan sanda suka buɗe masu wuta da harsasai masu rai.

Kara karanta wannan

Rana ta 2: Masu zanga zanga sun sake fitowa a Abuja, sun gamu da fushin ƴan sanda

Yan sanda sun kama ɓata-gari a Kano

A wani rahoton na daban, an ji rundunar 'yan sandan Kano ta bayyana karin nasara a kan bata-garin da suka saci kayan jama'a yayin zanga-zanga a ranar farko.

Jami'in hulda da jama'a na rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar da kamen bayan jami'an tsaro sun ci gaba da aikinsu.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262