"Tinubu Ba Masihirci Ba ne": Minista Ya Fadi Abin da Ya Dace 'Yan Najeriya Su Yi

"Tinubu Ba Masihirci Ba ne": Minista Ya Fadi Abin da Ya Dace 'Yan Najeriya Su Yi

  • Olabunmi Tunji-Ojo ya yi kira ga ƴan Najeriya su kai zuciya nesa, su ƙara ba shugaban ƙasa Bola Tinubu lokaci domin ya yi gyara a ƙasar nan
  • Ministan harkokin cikin gida ya bayyana cewa babu adalci a yi tsammanin cewa Tinubu zai magance matsalolin ƙasar nan cikin ƙanƙanin lokaci
  • Ya nuna cewa matsalolin da ake fama da su a ƙasar nan a yanzu, shugaban kasa Tinubu zuwa ya yi kuma ya gaje su domin dama can sun daɗe

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ya yi kira ga ƴan Najeriya da su ƙara ba Shugaba Bola Tinubu lokaci domin magance ƙalubalen tattalin arziƙin da ya addabi ƙasar nan.

Kara karanta wannan

Zanga zangar adawa da Tinubu: Minista ya yi magana mai kaushi, ya fadi kulla kullar da ake yi

Ministan ya kuma yi kira ga masu shirin fita zanga-zangar da za a gudanar a ranar 1 ga watan Agusta da su kasance masu kishin ƙasa.

Tunji Ojo ya bukaci a karawa Tinubu lokaci
Olabunmi Tunji-Ojo ya ce Tinubu na bukatar karin lokaci Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, Olabunmi Tunji-Ojo
Asali: Twitter

"Tinubu na buƙatar lokaci" - Tunji-Ojo

Olabunmi Tunji-Ojo ya bayyana hakan ne a yayin wata tattaunawa da gidan talabijin na Channels tv a ranar Lahadi.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ce bai kamata a yi tsammanin cewa Tinubu zai magance matsalar da ta shafe shekara 100 a cikin shekara ɗaya kacal ba.

Jaridar TheCable ta ce ministan ya nuna cewa matsalolin da ake fama da su a yanzu, sun samu ne sakamakon rashin iya gudanar da mulki a cikin shekara 100, 60, 30 da suka gabata.

"A iya abin da na sani, shugaban ƙasa bai taɓa kamfen cewa shi masihirci ne ba, ya yi kamfen ne a matsayin ɗan ƙasa, ya yi yaƙin neman zaɓe ne bisa manufar 'Renewed Hope'".

Kara karanta wannan

Tsadar rayuwa: Kashim Shettima ya ba 'yan Najeriya mafita maimakon yin zanga-zanga

"Idan ana son gyara abin da ya lalace, ana buƙatar lokaci, kuma muna kan gaɓar yin wannan gyaran."

- Olabunmi Tunji-Ojo

Matsayar ministan a kan zanga-zanga

Olabunmi Tunji-Ojo ya bayyana cewa kamata ya yi duk sai an gama bin hanyoyin tattaunawa domin samun maslaha kafin a fara zanga-zanga.

Ya nanata cewa Tinubu da alheri ya zo kuma ya ɗauki matakai masu kyau ciki har da cire tallafin man fetur wanda ya bayyana a matsayin annoba.

Ministan ya ƙara da cewa a yanzu Najeriya jinya take yi kuma za ta wartsake ta dawo cikin ƙoshin lafiya.

Diyar Tinubu ta magantu kan zanga-zanga

A wani labarin kuma, kun ji cewa ɗiyar shugaban ƙasa Bola Tinubu, Folashade Tinubu ta yi magana kan shirin zanga-zangar matasa a faɗin Najeriya.

Folashade wacce ta ja kunnen iyaye ta tabbatar da cewa babu wata zanga-zanga da za a yi a jihar Legas a ranar 1 ga watan Agustan 2024.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Jigon APC ya fadi abin da 'yan Najeriya ya kamata su yi wa Tinubu

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng