Zanga Zanga: 'Yan Sanda Sun Cafke Matashi Mai Kiran Jama'a Su Fito Kan Tituna

Zanga Zanga: 'Yan Sanda Sun Cafke Matashi Mai Kiran Jama'a Su Fito Kan Tituna

  • Wani matashi mazaunin garin Suleja a jihar Neja mai suna Wali Haruna ya faɗa hannun ƴan sanda bisa zargin tunzura jama'a
  • Matashin dai ya yi rubutu a Facebook inda ya yi kira da a fito zanga-zangar da ake shirin yi a faɗin ƙasar nan daga ranar, 1 ga watan Agusta
  • Kakakin rundunar ƴan sandan jihar, Wasiu Abiodun, ya tabbatar da cafke matashin inda ya ce ana ci gaba da yi masa tambayoyi

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Neja - Wani matashi mai suna Wali Haruna, mazaunin Suleja a jihar Neja, ya shiga hannun ƴan sanda kan kiran matasa su fito zanga-zanga.

Wali Haruna ya yi wani rubutu ne a Facebook yana kiran a shiga zanga-zangar da ake shirin yi a faɗin ƙasar nan.

Kara karanta wannan

Shehu Sani ya lissafo hanyoyi 6 da zanga zangar lumana ke komawa tashin hankali

'Yan sanda sun cafke matashi a Neja
Matashi mai kiran a fito zanga-zanga ya fada komar 'yan sanda a Neja Hoto: Anadolu Agency
Asali: Getty Images

Ƴan sanda sun cafke matashi a Neja

Jaridar Daily Trust ta ce ƴan sanda sun yi caraf da shi ne a gidansa da ke unguwar Kabula a Suleja ranar Juma’a kafin a miƙa shi zuwa sashen CID da ke Minna.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wani ɗan uwan matashin wanda ya nemi a sakaya sunansa ya bayyana cewa rubutun da ya yi ne a shafinsa na Facebook ya sanya aka kama shi, rahoton jaridar Sahara Reporters ya tabbatar.

Ya ce ya yi rubutu a Facebook, yana mai cewa “Za a iya yin zanga-zanga a Najeriya. Muna goyon hakan. Mu je zuwa"

Wadannan da sauran rubuce-rubucen da ya yi ne suka sanya ya faɗa komar ƴan sanda.

Me ƴan sanda suka ce kan lamarin?

Kakakin rundunar ƴan sandan jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da cafke matashin wanda ya yi kiran da a fito zanga-zanga.

Kara karanta wannan

Donald Trump ya tada hankalin duniya, ya fadi abin da zai faru idan bai ci zabe ba

“An gayyaci Wali Haruna mazaunin Suleja ne a ranar 26 ga watan Yuli, domin amsa tambayoyi bayan ya raba bayanan zanga-zanga a shafukan sada zumunta."

"Ana yi masa tambayoyi ne saboda ana zarginsa da tunzura jama’a su yi zanga-zanga da tabbatar da ko yana cikin wasu gungun mutane da ke shirin yin zanga-zanga da gano yadda za a gudanar da irin wannan zanga-zangar domin a yi taka tsantsan."

- SP Wasiu Abiodun

Karanta wasu labaran kan zanga-zanga

Zanga zanga: Kungiyar Amnesty Intl ta caccaki gwamnati kan kama ɗan gwagwarmayan Tiktok

Shehu Sani ya lissafo hanyoyi 6 da zanga zangar lumana ke komawa tashin hankali

Ana harin zanga zanga, gwamnatin tarayya ta dauki muhimmin mataki

Ƙungiya ta fice daga shiga zanga-zanga

A wani labarin kuma, kun ji cewa ƙungiyar ƴan asalin jihar Zamfara (ZIEF) ta sanar da janyewa daga zanga-zangar da aka shirya gudanarwa a faɗin ƙasar nan.

Kara karanta wannan

Rundunar ƴan sanda ta tona asiri, ta ce an ɗauko sojojin haya a zanga zangar da ake shiryawa

Ƙungiyar ta bayyana cewa ta ɗauki matakin ne saboda rashin sanin haƙiƙanin shugabannin da za su jagoranci zanga-zangar a ƙasa baki ɗaya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng