Gwamnatin Tinubu Ta Fadi Hanyar Magance Zanga Zangar da Ake Shirin Yi

Gwamnatin Tinubu Ta Fadi Hanyar Magance Zanga Zangar da Ake Shirin Yi

  • Gwamnatin tarayya ta yi kira ga masu shirin fitowa kan tituna da niyyar yin zanga-zanga su kwantar da hankulansu
  • Gwamnatin ta bayyana cewa shugaban ƙasa Bola Tinubu da ministocinsa na aiki tuƙuru domin ganin sauƙi ya samu a ƙasar nan
  • Ministan yaɗa labarai wanda ya bayyana hakan, ya ce zanga-zangar lamari ne na cikin gida wanda za a warware domin a samu ci gaba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Gwamnatin tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Tinubu ta yi kira ga masu shirin gudanar da zanga-zanga a faɗin ƙasar nan saboda matsalar karancin abinci da yunwa, da su kwantar da hankalinsu.

Gwamnatin ta buƙace su da su rungumi zaman lafiya, tana mai cewa shugaban ƙasa Bola Tinubu da ministocinsa na ƙoƙarin sauya lamarin.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Tinubu ta bayyana dalilin da ya sa ba ta son a yi zanga zanga

Gwamnatin Tinubu ta roki masu shirin zanga-zanga
Gwamnatin tarayya ta bukaci masu shirin yin zanga-zanga su kwantar da hankulansu Hoto: Ajuri Ngelale
Asali: Facebook

Ministan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed Idris, ya bayyana hakan bayan kammala taron majalisar zartaswa ta tarayya a Abuja, cewar rahoton jaridar Leadership.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ministan ya jaddada cewa gwamnati na aiki tuƙuru domin warware matsalolin da ake fuskanta, rahoton jaridar The Nation ya tabbatar.

Me gwamnatin Tinubu ta ce kan zanga-zanga?

Mohammed Idris ya bayyana zanga-zangar da aka shirya a matsayin "lamarin cikin gida" wanda za a warware domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasa.

"Waɗanda suke son yin zanga-zanga ƴan uwanmu ne. Wannan lamari ne da ya shafi Najeriya, kuma muna lura da shi da kyau, muna fatan za a samu zaman lafiya."
"Shugaban ƙasa da sauran manyan jami'an gwamnati suna ta ganawa da masu ruwa da tsaki. Wannan ita ce ƙasa ɗaya tilo da muke da ita, kuma mun yi amanna cewa Najeriya za ta gyaru.

Kara karanta wannan

Jigon APC ya fadi abin da ya kamata a yiwa Tinubu yayin da ake harin zanga-zanga

Shugaban ƙasa da ministocinsa suna aiki tuƙuru. Dukkanmu muna saurare, kuma saƙon shugaban ƙasa kodayaushe shi ne ku kwantar da hankali ku ƙara mana lokaci. Za a magance dukkanin buƙatun ku."

- Mohammed Idris

Karanta wasu labaran kan zanga-zanga

Jigon APC ya ba ƴan Najeriya shawara

A wani labarin kuma, kun ji cewa wani jigon jam’iyyar APC a jihar Ondo, Dakta Femi Adekanmbi, ya yi magana kan zanga-zangar da ake shirin yi.

Jigon na APC ya yi kira ga matasan Najeriya da su janye zanga-zangar da suke shirin yi a fadin ƙasar nan saboda halin ƙuncin da ake ciki.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng