UTME: Jerin Sunaye da Jihohin Ɗaliban da Suka Yiwa Jarabawar JAMB Cin Kaca a 2024

UTME: Jerin Sunaye da Jihohin Ɗaliban da Suka Yiwa Jarabawar JAMB Cin Kaca a 2024

  • Hukumar JAMB ya bayyana sunayen ɗaliban da suka ci maki mafi yawa a jarabawar share fagen shiga jami'a ta bana 2024
  • Shugaban JAMB na kasa, Farfesa Ishaq Oloyede ne ya sanar da sunayen ɗaliban a wurin taron majalisar gudanarwa ta hukumar a Abuja
  • Wannan na zuwa ne yayin da gwamnatin tarayya ta yi amai ta lashe kan mafi ƙarancin shekarun shiga jami'a a Najeriya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Hukumar shirya jarabawar share fagen shiga jami'o'i a Najeriya (JAM) ta saki sakamakon jarabawar da ɗalibai suka zauna a faɗin kasar da wasu ƙasashen waje.

Kamar yadda aka saba a kowace shekara, JAMB ta kuma fitar da jerin ɗaliban da suka nuna hazaƙa da ƙwazo suka samu maki mafi yawa a jarabawar UTME 2024.

Kara karanta wannan

JAMB ta sanar da sabon mafi karancin makin shiga manyan makarantu a Najeriya

Dakin zana jarabawar JAMB.
JAMB ta saki jerin sunayen ɗaliban da suka nuna bajinta a jarabawar bana Hoto: JAMB
Asali: Facebook

Shugaban hukumar JAMB na kasa, Farfesa Ishaq Oloyede ne ya bayyana ɗaliban da suka suka yiwa jarabawar cin kaca, kamar yadda Punch ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wannan na zuwa ne yayin da ministan ilimi, Tahir Mamman ya yi amai ya lashe kan mafi ƙarancin shekarun shiga jami'a a Najeriya

A farko, ministan ya bayyana cewa daga yanzu sai ɗalibi ya cika shekara 18 sannan za a ba shi gurbin karatu a jami'o'in ƙasar nan.

Sai dai nan take masu ruwa da tsaki suka yiwa matakin bore, lamarin ya sa Farfesa Tahir ya janye kalamansa tare da ayyana shekaru 16 a matsayin mafi karancin shiga jami'a.

Sunayen waɗanda suka fi samun makin JAMB

Farfesa Ishaq Oloyede ya bayyana sunayen ɗaliban da suka fi samun makin JAMB da jihohin da suka fito a wurin taron majalissr gudanarwa ta JAMB a Abuja yau Alhamis, Leadership ta rahoto.

Kara karanta wannan

Ganduje ya yi kamu, babban jigon da ya yaƙi tikitin Musulmi da Musulmi ya koma APC

Ga su kamar haka:

S/NSunayeMakiJiha
1⁠Olowu David367Ondo
2⁠⁠Alayande David367Oyo
3⁠⁠Orukpe Joel367Edo
4⁠⁠Emmanuel Jeremiah366Akwa Ibom
5⁠⁠Essiet Etini365Akwa Ibom
6⁠Ezenwoko Zara365Abia
7⁠⁠Umoh Joshua365Akwa Ibom
8⁠⁠Mamudu Abdulraham364Edo
9⁠⁠Adeleke Abdulbasit363Kwara
10Echem Victor363Ribas
11Etute Emmanuel363Edo
12Jedidiah Chidiebube363Imo
13Adesanya Oluwatimilehin363Ogun

JAMB ta gano masu ƙaryar takardu

A wani rahoton kuma kun ji cewa hukumar JAMB ta bayyana gano wasu masu karyar kammala manyan makarantu a Najeriya

Shugaban hukumar, Farfesa Ishaq Oleyede da ya bayyana haka ya kara da cewa matasa 3000 na rike da shaidar kammala makarantun.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262