Shehin Malami ya Musanta Karbar N16m daga Tinubu, ya Fadi Dalilin Ziyartar Shugaban Kasa

Shehin Malami ya Musanta Karbar N16m daga Tinubu, ya Fadi Dalilin Ziyartar Shugaban Kasa

  • Malaman addinin musulunci na ta karin bayani kan batun zanga-zanga da matasan kasar nan ke shirin gudanar wa
  • Sheikh Ishaq Adam Ishaq ya ce zagin malamai da ake yi ana zaton sun karbo na goro daga shugaba Bola Tinubu kuskure ne
  • Malamin ya ce babu malamin da aka zauna da shi a kan batun zanga zanga ballantana a yi maganar karbar toshiyar baki

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Najeriya - Shehin malami, Barista Ishaq Adam Ishaq ya musanta labarin cewa malamai sun karbi kudi har Naira Miliyan 16 daga shugaba Bola Ahmed Tinubu.

A wani bidiyon malamin, an jiyo shi ya na cewa babu yadda za a yi shugaban kasa da ya rika tura wa wani kudi kai tsaye kamar yadda ake yayata wa.

Kara karanta wannan

Riga malam masallaci: An hango allon kamfen Bola Tinubu na zaben 2027

Malamai
Barista Ishaq ya musanta cewa malamai sun karbi cin hanci domin haramta zanga-zanga Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu/Sheikh Barr. Ishaq Adam Ishaq
Asali: Facebook

Sheikh Ishaq Adam Ishaq ta cikin bidiyon da @el_uthmaan ya wallafa, ya ce zalunci ne a rika danganta malamai, ciki har da na ahlus sunnah da karbar kudi ana zaginsu a gari.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gaskiya kan zaman malamai da Tinubu

Shiekh Ishaq Adam Ishaq ya bayyana cewa malamai sun ziyarci fadar shugaban kasa ne domin tattaunawa a kan batun yarjejeniyar SAMOA.

Malamin ya ce sun bukaci shugaban kasa da a tabbata Najeriya ta fita daga wannan yarjejeniya saboda illarta ga jama'a, kamar yadda ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Ya ce rashin adalci ne a rika yada labarin karya ana cewa sun zauna ne domin karbar kudi saboda su yi fatawar haramta zanga-zanga a Najeriya.

"Tsoronmu kan zanga zanga," Sheikh Ishaq

Malamin addinin musulunci, Sheikh Ishaq Adam Ishaq ya bayyana fargabar da su ke da shi a kan zanga-zangar da matasan kasar nan ke shirin gudanarwa.

Kara karanta wannan

Bayan sun hana zanga zanga, malamai sun fara maganar ganin Tinubu domin samun mafita

Malamin ya ce a duba kasashen da su ka yi makamanciyar zanga-zangar a da, da halin da su ke ciki a yanzu, kamar yadda ya buga misali da Libya, Sudan da Syria.

"Lallai masu tsarin zanga-zangar nan su sani, ba wai malamai sun ce zanga-zanga haramun ce saboda son zuciya ba.."

- Shiekh Ishaq Adam Ishaq

Zanga zanga: Sheikh Maqari ya fadi matsayarsa

A baya kun ji cewa shehin malamin nan, Farfesa Ibrahim Maqari ya bayyana matsayarsa a kan zanga-zangar da matasa ke shirin gudanar wa.

Malamin ya ce duk da ba za a haramta zanga-zanga da sunan addinin musulunci ba, amma matasan kasar nan ba su shirya yin ta ba.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.