Babban Dan Tsohon Gwamna a Najeriya Ya Riga Mu Gidan Gaskiya

Babban Dan Tsohon Gwamna a Najeriya Ya Riga Mu Gidan Gaskiya

  • An shiga jimami bayan rasuwar babban ɗan tsohon gwamnan jihar Oyo, Cif Kolapo Ishola a yau Laraba a jihar
  • Marigayin mai suna Kunle Kolapo an tabbatar ya rasu ne da safiyar yau Laraba 3 ga watan Yulin 2027 a jihar
  • Rahotanni sun tabbatar da cewa marigayin babban ɗan tsohon gwamnan ne da ya mulki jihar daga 19991 zuwa 1993

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Oyo - Rahotanni da muke samu sun tabbatar da mutuwar babban ɗan tsohon gwamnan jihar Oyo, Kolapo Ishola.

Marigayin da ake kira Kunle Kolapo ya rasu da safiyar yau Laraba 3 ga watan Yunin 2024.

Dan tsohon gwamna a Najeriya ya kwanta dama
Babban dan tsohon gwamnan Oyo, Kunle Kolapo ya rasu. Hoto: Olutoyin Adeyinka Eweje.
Asali: Facebook

Oyo: Yaushe marigayin ya rasu?

Kara karanta wannan

Gidan tsohon gwamna, Okorocha ya ruguje, katafaren gini ya danne mutane a Abuja

Leadership ta tattaro cewa marigayin kafin rasuwarsa lauya ne kuma ya tsohon kwamishina a jihar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kunle ya rike mukamin kwamishinan ne a mulkin tsohon gwamnan jihar, Otunba Christopher Alao-Akala.

Har zuwa lokacin tattara wannan rahoto ba a bayyana musabbabin mutuwar babban ɗan tsohon gwamnan ba.

Har ila yau, iyalan basu fitar da wata sanarwa ba a hukumance kan babban rashin da suka tafka.

Mulkin tsohon gwamnan Oyo, Kolapo

Tsohon gwamnan ya mulki jihar Oyo ne daga shekarar 1991 zuwa 1993 a karkashin jam'iyyar SDP.

Ishola da aka haifa a watan Yunin 1934 ya jagoranci jihar ne a Jamhuriya ta uku wanda ya kawo ayyukan ci gaba musamman a bangaren ilimi.

Marigayin ya bar ofis ne a ranar 17 ga watan Nuwambar 1993 lokacin da marigayi Janar Sani Abacha ya hau mulki.

Daga bisani, Ishola ya rasu a ranar 9 ga watan Agustan shekarar 2011 yana da shekaru 77 a duniya.

Kara karanta wannan

An shiga jimamin mutuwar wata Farfesa cikin wani yanayi maras dadi a gidanta a Maiduguri

Matashi ya hallaka mahaifinsa a Delta

A wani labarin, kun ji cewa wani matashi mai suna Ufuoma ya hallaka mahaifinsa wanda Fasto ne a jihar Delta.

Marigayin mai suna Issac Umurie ya rasa ransa ne yayin da yake tsaka da barci da tsakar daren yau Laraba 3 ga watan Yulin 2024.

Matashin har ila yau, ya farmaki mahaifiyarsa yayin da take kokarin kare mijinta da kuma dakatar da shi daga aikata hakan.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Online view pixel