Fadar Sarkin Musulmi Ta Bayyana Gaskiya Kan Rigima da Gwamnatin Sokoto

Fadar Sarkin Musulmi Ta Bayyana Gaskiya Kan Rigima da Gwamnatin Sokoto

  • Fadar Sarkin Musulmi ta fito ta yi magana kan batun da ake yaɗawa cewa akwai saɓani a tsakaninta da gwamnatin jihar Sokoto
  • Fadar ta bayyana cewa babu wata matsala a tsakanin mai alfarma Alhaji Sa'ad Abubakar III da gwamnan jihar Sokoto, Alhaji Ahmed Aliyu
  • Sa'in Kilgoro wanda ya tabbatar da hakan ya ce a shirye fadar Sarkin Musulmin take ta yi aiki da sabuwar dokar da ake ƙoƙarin kawowa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Sokoto - Daga ƙarshe fadar Sarkin Musulmi ta yi magana kan batun gyaran dokar ƙananan hukumomin jihar Sokoto ta shekarar 2008.

Sa’in Kilgori, Dakta Muhammad Jabbi Kilgori, ya ce gyaran da za a yiwa dokar ba zai ƙwace iko ko rage ƙarfin da Sarkin Musulmin yake da shi ba.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Sokoto ta fadi dalilin yin doka domin rage ikon Sarkin Musulmi

Fadar Sarkin Musulmi ta musanta samun sabani da gwamnan Sokoto
Fadar Sarkin Musulmi ta shirya aiki da sabuwar doka a Sokoto Hoto: @AhmedAliyuSkt
Asali: Twitter

Jaridar Daily Trust ta ce ya bayyana hakan ne yayin da yake magana a wajen buɗe taron jin ra'ayin jama'a kan gyaran da za a yiwa dokar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Akwai matsala tsakanin Sarkin Musulmi da gwamna?

Ya bayyana cewa saɓanin abin da ake yaɗawa, babu wata matsala tsakanin Sarkin Musulmi, Alhaji Sa'ad Abubakar III da gwamnan jihar Sokoto, Alhaji Ahmed Aliyu.

Jaridar Tribune ta ce Muhammad Kilgori, wanda yake da muƙamin Hakimin Kilgori kuma 'dan majalisar Sarkin Musulmi, ya ce fadar na sane da wasu maƙiya masu son kawo matsala tsakanin Sarkin Musulmi da gwamnatin jihar.

"Babu wata matsala tsakanin Sarkin Musulmi da Gwamna Ahmed Aliyu. Majalisar Sarkin Musulmi a shirye take ta yi aiki da kowace doka wacce aka samar ta hanyar da ta dace."
"Mun yi aiki da dokoki daban-daban a baya kuma a shirye muke mu yi aiki da wannan sabuwar dokar."

Kara karanta wannan

Tsohon jigon APC ya wanke Tinubu kan halin da Arewa ke ciki, ya fadi mai laifi

"Majalisar Sarkin Musulmi ta yi aiki a ƙarƙashin dokar da ake shirin yiwa gyara na tsawon shekara 16. A shirye muke mu yi aiki tare da gwamnati."

- Dakta Muhammad Jabbi Kilgori

Batun tsige Sarkin Musulmi

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnatin jihar Sokoto ta musanta zargin da MURIC ta yi na cewa tana shirin tsige mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III.

Ta kuma buƙaci mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima da ya riƙa bin diddigin gaskiya kafin ya yi tsokaci kan wasu muhimman batutuwan da ke faruwa a ƙasa.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng

Online view pixel