'Yan Bindiga Sun Yiwa Jami'an Tsaro Kwantan Ɓauna, An Rasa Rayuka a Katsina

'Yan Bindiga Sun Yiwa Jami'an Tsaro Kwantan Ɓauna, An Rasa Rayuka a Katsina

  • Ƴan bindiga sun yiwa ayarin jami'an tsaro kwantan ɓauna a yankin ƙaramar hukumar Jibia da ke jihar Katsina da safiyar ranar Lahadi
  • Rahotanni sun bayyana cewa ƴan ta'addan sun kashe ƴan sanda huɗu nan take, sannan wani ɗaya ya rasu bayan an kai shi asibiti
  • Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar, ASP Abubakar Aliyu ya ce a saurare shi amma har kawo yanzu bai fitar da sanarwa a hukumance ba

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Katsina - 'Yan bindiga sun kashe jami’an ‘yan sanda biyar a wani harin kwantan bauna da suka kai a karamar hukumar Jibia da ke jihar Katsina.

Mazauna yankin sun ce lamarin ya faru ne da safiyar Lahadi a yayin da ƴan sandan ke hanyar zuwa cikin garin Jibia daga sansaninsu da ke kauyen Zandam.

Kara karanta wannan

'Yan Boko Haram sun kwararo zuwa jihar Neja daga kasashen waje? An gano gaskiya

Sufetan ƴan sanda, IGP Kayode.
Yan bindiga sun kashe yan sanda 5 a Jibia da ke Katsina Hoto: PoliceNG
Asali: Twitter

'Yan bindiga sun hallaka 'yan sanda

Jaridar Premium Times ta tattaro cewa ƴan sanda huɗu sun mutu ne nan take a wurin yayin da ɗan sanda ɗaya ya ƙarisa a asibitin FMC da ke Katsina.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Bayanai sun nuna cewa ƴan ta'addan sun sace bindigun AK47 guda biyar bayan sun kashe jami'an tsaron da misalin ƙarfe 6:00 na safiyar ranar Lahadi.

Wane mataki hukumomi suka ɗauka?

Jami'in hulɗa da jama'a na rundunar ƴan sandan jihar Katsina, ASP Abubakar Aliyu ya ce zai yi magana nan ba da jimawa ba idan ya gama tattara bayanai.

Sai dai har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton bai fitar da wani ƙarin bayani ba amma wani rahoton tsaro ya tabbatar da faruwar lamarin, rahoton Guardian.

Rahoton tsaron ya bayyana wurin da aka kai harin a matsayin wuri mai hadarin gaske kuma ya gargadi jami’an ‘yan sanda su gujewa bin wannna titin.

Kara karanta wannan

Jirgin sojojin saman Najeriya ya yi hatsari, dakaru sun hallara a kauyen Kaduna

Ƴan bindiga dai na yawan kai hare-hare a yankin ƙaramar hukumar Jibia ta jihar Katsina da kuma garuruwan da ke makwaftaka da jihohin Zamfara da Kaduna.

An sace basarake a Kaduna

A wani rahoton, 'yan bindiga sun yi awon gaba da dagacin Tunburku, Malam Ashiru Sharehu a ƙaramar hukumar Giwa ta jihar Kaduna.

Mazauna garin sun bayyana cewa maharan sun tafi da basaraken a lokacin da ya kamo hanyar dawowa gida daga gonarsa ranar Asabar.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel