"Za Mu Bi Tsarinmu," Gwamna Ya Faɗi Shirinsa Kan Sabon Mafi Ƙarancin Albashi

"Za Mu Bi Tsarinmu," Gwamna Ya Faɗi Shirinsa Kan Sabon Mafi Ƙarancin Albashi

  • Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa ya ce har yanzu gwamnatin jihar ba ta yanke adadin da zata biya a mataayin sabon mafi karancin albashi ba
  • Namadi ya bayyana cewa gwamnatin Jigawa ba ta ma fara tattaunawa kan ƙarin albashi da ƙungiyar kwadago ta jihar ba
  • Ya ce zai sanar da sabon mafi ƙarancin albashin da gwamnatinsa za ta yi amfani da shi bayan zama da ƴan kwadago

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Dutse, jihar Jigawa - Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa ya bayyana shirinsa kan sabon mafi ƙarancin albashin ma'aikata a jihar.

Namadi ya ce bai dame shi ko nawa gwamnatin tarayya ta yanke a matsayin mafi ƙarancin albashi ba amma gwamnatinsa za ta tattauna da ma'aikata kan lamarin.

Kara karanta wannan

"Talauci zai ƙaru a Najeriya": NLC ta gargaɗi gwamnoni kan yanke mafi ƙarancin albashi

Umar Namadi.
Gwamnatin Umar Namadi za ta zauna da ma'aikata kan sabon mafi karancin albashi a Jigawa Hoto: Jigawa state Radio
Asali: Facebook

Gwamnan ya bayyana haka ne yayin da yake jawabi a cikin shirin Sunrise Daily na gidan talabijin na Channels ranar Jumu'a, 28 ga watan Yuni, 2028.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Idan baku manta ba gwamnatin tarayya karkashin Bola Ahmed Tinubu ta miƙa tayin N62,000 ga ƴan kwadago a lokacin tattaunawa kan ƙarin albashin.

Amma da yake tsokaci kan lamarin, Gwamna Namadi ya ce a al'adar jihar Jigawa wajibi ne masu ruwa da tsaki da ƴan kwadago su zauna su yanke adadin da za a biya.

Gwamna Namadi ya faɗi shirinsa a Jigawa

Ya ce Jigawa ba ta amince da wani adadi a matsayin sabon mafi karancin albashi ba saboda ba su fara tattaunawa da ma’aikata a jihar ba har kawo yanzu.

"Ba zamu ce ga abin da zamu biya ba a yanzu saboda lamari ne na tattaunawa, Jigawa ba ta amince da wani adadi ba, a taƙaice ma bamu fara zaman ba.

Kara karanta wannan

NLC: Bola Tinubu ya samu saƙon mafita kan mafi ƙarancin albashi a Najeriya

"Zamu haɗa kwamiti da ya ƙunshi masu ruwa da tsaki da ƴan kwadago kuma mu yi aiki tare wanda a ƙarshen zamu cimma matsaya kan adadin da ya dace."

- Gwamnan Jigawa, Umar Namadi Ɗanmodi.

Gwamnoni sun gana kan karin albashi

A wani rahoton na daban Gwamnoni 36 na Najeriya sun tabbatar da cewa ma'aikata za su samu ƙarin albashi mai tsoka a tattaunawar da ake yi

AbdulRahman AbdulRazaq na jihar Kwara ne ya bayyana haka bayan taron ƙungiyar gwamnoni wanda ya gudana ranar Laraba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel