Lokaci Ya Yi: Kwamishinan Bauchi Ya Rasu Yana da Shekara 60 a Duniya

Lokaci Ya Yi: Kwamishinan Bauchi Ya Rasu Yana da Shekara 60 a Duniya

  • Allah ya yiwa kwamishinan ƙananan hukumomi da masarautu na jihar Bauchi rasuwa a ranar Asabar, 1 ga watan Yunin 2024
  • Ahmed Jalam ya rasu ne tare da direbansa a wani hatsarin mota da ya ritsa da su lokacin da yake kan hanyar zuwa garinsa na Jalam
  • Gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, ya aike da saƙon ta'aziyyarsa inda ya bayyana rasuwar kwamishinan a matsayin babban rashi

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Bauchi - Kwamishinan ƙananan hukumomi da masarautu na jihar Bauchi, Ahmed Jalam ya rasu.

Marigayin ya rasu ne tare da direbansa a wani hatsarin mota da ya rutsa da su a hanyar babban titin Bauchi/Jalam a ranar Asabar, 1 ga watan Yunin 2024.

Kara karanta wannan

Hantar Tinubu ta ƙaɗa, Shugaban PDP ya faɗi yadda za a kayar da APC a zaɓen 2027

Ahmed Jalam ya rasu
Ahmed Jalam ya rasu yana da shekara 60 Hoto: Ahmed Jalam
Asali: Facebook

An bayyana cewa suna kan hanyarsu ta zuwa garin Jalam ne a ƙaramar hukumar Dambam a lokacin da hatsarin ya auku, cewar rahoton jaridar The Punch.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnan Bauchi ya yi ta'aziyya

Da yake miƙa saƙon ta'aziyyarsa, gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, ya bayyana rasuwar Ahmed Jalam a matsayin wani babban rashi.

Gwamnan ya bayyana cewa rasuwarsa ta bar giɓi saboda jajircewarsa wajen yiwa al'umma hidima, rahoton jaridar Daily Trust ya tabbatar.

“Mutuwar kwamishinan ta bar babban giɓi a jihar kuma ta jefa mutanen jihar cikin alhini saboda yadda ya yi suna wajen sadaukar da kai da jajircewarsa wajen yin hidima."
"Ahmad Jalam ya riƙe muƙamin kwamishinan harkokin addini a shekarar 2019 kuma an sake naɗa shi matsayin kwamishina a shekarar 2023 kuma ya yi aiki a ma'aikatar ƙananan hukumomi da masarautu har zuwa ƙarshen rasuwarsa."

Kara karanta wannan

Matawalle ya dauki zafi kan kisan sojoji a Abia, ya fadi matakin dauka

- Sanata Bala Mohammed

Kwamishinan ya rasu yana da shekaru 60 a duniya kuma ya bar mata da ƴaƴa.

Za a yi sallar jana’izarsa a safiyar ranar Lahadi, 2 ga watan Yuni kamar yadda addinin Musulunci ya tanada a garinsu na Jalam.

Wani Alhaji ya rasu a Saudiyya

A wani labarin kuma, kun ji cewa ɗaya daga cikin alhazan jihar Legas mai suna, Idris Oloshogbo, ɗan kimanin shekaru 68 a duniya ya rasu a ƙasa mai tsarki.

Likitocin ƙasar Saudiyya ne suka tabbatar da rasuwar Alhaji Oloshogbo a birnin Makkah bayan ya dawo daga Ɗawafin Ka'abah.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng