'Yan Bindiga da Yawa Sun Baƙunci Lahira Yayin da Suka Kai Hari a Jihar Arewa, Mutum 2 Sun Tsira
- Tsagerun masu garkuwa da mutane 3 sun bakunci ƙahira yayin musayar wuta da ƴan sanda a jihar Adamawa
- Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar, SP Suleiman Nguroje, ya ce dakarun sun ceto mutum 3 da maharan suka sace
- Ya ce lamarin ya faru ne bayan masu garkuwan sun kai hari wurin kiwon wani mutumi, inda suka tafi da mutum 2
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Jihar Adamawa - Wasu miyagun ƴan bindiga 3 masu garkuwa da mutane sun baƙunci lahira a jihar Adamawa da ke shiyyar Arewa maso Gabashin Najeriya.
Jaridar The Nation ta tattaro cewa dakarun ƴan sanda ne suka sheƙe su a wani samame da suka kai tare da taimakon mafarauta ƴan sa'kai.

Kara karanta wannan
Filato: Asirin wasu mutane da ake zargi da hannu a kashe bayin Allah sama da 100 ya tonu a Arewa

Source: Facebook
Yayin wannan samame da jami'an tsaron suka fita, sun yi nasarar ceto mutum biyu da ƴan bindigan suka yi garkuwa da su, Daily Post ta ruwaito.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Jami'in hulɗa da jama'a na rundunar ƴan sandan jihar Adamawa, SP Suleiman Nguroje, ne ya tabbatar da haka a wata sanarwa ranar Alhamis, 25 ga watan Janairu.
Ya ce ranar Laraba, 24 ga watan Janairu, 2024, ‘yan sanda suka ragargaji kungiyar miyagun a tsaunin Koma mai hade da garuruwan Kojoli da Karlahi na kananan hukumomin Jada da Fufore a Adamawa.
Yan sanda sun ceto mutum da aka sace
Kakakin ƴan sandan ya ci gaba da cewa:
"Jiya Laraba, masu garkuwa suka kai hari a wani wurin kiwon shanu na Alhaji Jibo Karlahi inda suka tafi da Umar Jibo mai shekaru 18 da Idi Hassan mai shekaru 13 a duniya.

Kara karanta wannan
Babbar Nasara: Ƴan sanda sun yi kazamin artabu da ƴan bindiga, sun ceto mutane a FCT
"Nan take rundunar ƴan sanda ta tashi tawagar ceto suka bi sawun maharan. Daga ganin dakarunmu sai suka buɗe wuta aka fara musayar wuta. Sakamakon haka muka kashe 3 daga cikinsu.
"Amma sauran sun ari na kare ɗauke da raunukan harbin bindiga, abin farin cikin mun yi nasarar ceto mutum 2 da suka sato ba tare da an cutar da su ba."
A cewarsa, wannan nasara na ɗaya daga cikin ƙoƙarin rundunar na magance aikata manyan laifuka da suka haɗa da garkuwa, satar shanu, fashi da sauransu a jihar.
Sojoji sun gano abubuwan da suka haddasa rikicin Mangu
A wani rahoton kun ji cewa Rundunar sojojin Najeriya ta bayyana muhimman abu 2 da suka jawo tashe-tashen hankulan da ke faruwa a Mangu, jihar Filato.
Kakakin hedkwatar tsaro, Janar Buba, ya ce kisan da wani makiyayi ya yi wa ɗan garin Mangu na cikin abubuwan da suka jawo rikicin.
Asali: Legit.ng