Ana Zanga-Zanga a Kano Kan Tsige Abba Gida Gida, Bidiyo Ya Bayyana
- Zanga-zanga ta barke a jihar Kano bayan tsige Gwamna Abba Yusuf da kotun daukaka kara ta yi
- Hakan ya kasance ne yayin da yan sanda suka tarwatsa masu zanga-zangar a yankin Dan Agundi da ke jihar a ranar Laraba, 22 ga watan Nuwamba
- Zanga-zangar ta biyo bayan sakin kwafin shari'ar CTC wacce ta sha bamban da hukuncin kotun daukaka kara
Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amuran yau da kullum
Jihar Kano - Magoya bayan jam'iyyar NNPP sun mamaye titunan jihar Kano a ranar Laraba, 22 ga watan Nuwamba, domin yin zanga-zanga kan kayen da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sha a kotun daukaka kara.
Daga bisani jami’an yan sandan Najeriya sun tarwatsa masu zanga-zangar ta hanyar harba barkonon tsohuwa.

Asali: Twitter
APC vs NNPP: Zanga-zanga ya barke a Kano
Jaridar Daily Trust da Channels TV ma sun fitar da rahotanni kan zanga-zangar.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Zanga-zangar ta biyo bayan sakin kwafin shari'ar CTC wacce ta sha bamban da hukuncin kotun daukaka kara.
Wasu daga cikin masu zanga-zangar sun ce a shirye suke su mutu yayin da suke neman adalci.
Ga bidiyon zanga-zangar a kasa:
Kotu ta saki takardun hukuncin shari'ar Kano
A baya mun ji cewa kwanaki biyar bayan yanke hukunci, kotun daukaka ƙara ta saki takardun hukuncin shari'ar gwamnan Kano da ta yanke.
Kotun ɗaukaka ƙarar ta yanke hukuncin ne a kan zaɓen gwamnan jihar Kano da ake takaddama a kai a ranar Juma'a, 17 ga watan Nuwamba, inda ta ba jam'iyyar APC da ɗan takararta, Nasiru Gawuna, nasara.

Kara karanta wannan
Kano: Yayin da CTC ta tabbatar da nasarar Abba Kabir, NNPP ta fadi hanyar warware matsalar
Salihu Tanko Yakasai, wanda aka fi sani da Dawisu, ɗan takarar gwamnan jihar Kano a ƙarƙashin jam'iyyar PRP a zaɓen 2023 ne ya sanya takardun na CTC a shafinsa na X (wanda a baya aka fi sani da Twitter).
NNPP ta magantu kan shari'ar Kano
A gefe guda, jami'yyar NNPP ta yi martani kan rikita-rikitar da ke cikin hukuncin kotun daukaka a zaben gwamnan Kano.
Idan ba a manta ba a jiya Talata aka saki kwafin shari'ar ta CTC wacce ta sha bamban da hukuncin kotun daukaka kara, cewar Punch.
Asali: Legit.ng