Tinubu Ya Sallami Shugabannin NBC, NAN Da NTA, Ya Nada Sabbi

Tinubu Ya Sallami Shugabannin NBC, NAN Da NTA, Ya Nada Sabbi

  • Shugaba Bola Tinubu ya yi sabbin nade-nade a Ma’aikatar Yada Labarai da Hukumar Wayar da Kan Jama’a
  • Tinubu ya yi sabbin nade-naden ne har guda takwas wadanda za su yi aiki karkashin ma’aikatar Yada Labarai
  • Hadimin shugaban a bangaren kafar sadarwa ta zamani, David Olusegun shi ya bayyana haka a yau Alhamis ashafin Twitter

FCT, Abuja – Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya yi sabbin nade-nade a Ma’aikatar Yada Labarai da Hukumar Wayar da Kan Jama’a (NOA).

Tinubu ya nada Mista Lanre Issa Onilu a matsayin shugaban Hukumar ta NOA yayin da ya nada Salihu Abdulhamid Dembos shugaban Gidan Talabijin na Kasa, NTA.

Tinubu ya sallami shugabannin NTA, NAN, VOA da saura, ya nada sabbi
Tinubu Ya Sallami Shugabannin NBC, NAN Da NTA. Hoto: Bola Ahmed Tinubu.
Asali: Twitter

Su waye Tinubu ya nada a hukumomin?

Hadimin shugaban a bangaren kafar sadarwa ta zamani, David Olusegun shi ya tabbatar da haka a shafinsa a Twitter a yau Alhamis 19 ga watan Oktoba.

Kara karanta wannan

Da Dumi-Dumi: Majalisar Dattawa Ta Bi Umarnin Tinubu, Ta Tabbatar a Nadin Manyan Mukaman da Ya Tura

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tinubu ya nada mutane takwas a hukumomin wanda za su yi aiki karkashin ma’akatar Yada Labarai.

Sanarwar ta ce:

"Shugaba Tinubu ya nada sabbin shugabanni a ma'aikatar yada labarai ta kasa."

Legit Hausa ta jero muku jerin sabbin nade-naden:

1. Mista Lanre Issa Onilu - shugaban hukumar NOA

2. Mista Salihu Abdulhamid Dembos - shugaban NTA

3. Dakta Mohammed Bulama - shugaban hukumar FRCN

4. Mista Charles Ebuebu - shugaban hukumar NBC

5. Jibrin Baba Ndace - shugaban hukumar VON

6. Dakta Lekan Fadolapo - shugaban hukumar ARCON

7. Ali Mohammed Ali - shugaban hukumar NAN

8. Mista Dili Ezughan - shugaban hukumar NPC."

Wane gargadi Tinubu ya yi ga sabbin nade-naden?

Tinubu ya bukaci sabbin shugabannin da su yi aiki don kawo sauyi a hukumominsu daban-daban, Legit ta tattaro.

Tinubu ya kuma bukace su da su yi iya yinsu don ganin sun hada kan 'yan kasar da sauya tunanin mutane da kuma daga martabar kasar a idon duniya.

Kara karanta wannan

Ruwan Nadin Mukaman Tinubu Ya Shiga SON, An Nada Sabon Shugaba a Najeriya

Wannan na zuwa ne bayan shugaba Tinubu ya nada sabon shugaban hukumar ICPC, Dakta Adamu Aliyu Musa a ranar Talata 17 ga watan Oktoba.

Majalisa ta tabbatar da nadin shugaban EFCC, NSIPA

A wani labarin, majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin shugaban hukumar EFCC da NSIPA a jiya Laraba.

Majalisar ta amince da nadin Ola Olukoyede da Halima Shehu a matsayin shugabannin hukumomin.

Har ila yau, majalisar ta kuma tabbatar da mukamin sakataren Hukumar EFCC, Mohammed Hammajoda.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.