Gwamnatin Jihar Abia Ta Musanta Batun Korar Ma'aikata 10,000 Daga Aiki

Gwamnatin Jihar Abia Ta Musanta Batun Korar Ma'aikata 10,000 Daga Aiki

  • Gwamnatin jihar Abia ta musanta batun cewa ta datsewa ma'aikata 10,000 hanyar neman samun na cin abincinsu
  • Gwamnatin ta bayyana cewa ma'aikatan da aka sallama na bogi ne da waɗanda ba a bi ƙa'ida ba wajen ɗaukarsu aiki
  • Kwamishinan watsa labaran jihar Okey Kanu wanda ya tabbatar da hakan ya bayyana cewa ma'aikatan an saɓa ƙa'idoji wajen ɗaukarsu aiki

Jiihar Abia - Gwamnatin jihar Abia ta musanta rahotannin cewa ta kori ma'aikata 10,000 daga aiki.

Kwamishinan al'adu da watsa labarai na jihar, Okey Kanu, shi ne ya bayyana hakan a yayin wata tattaunawa da manema labarai a ranar Laraba, 6 ga watan Satumban 2023, rahoton PM News ya tabbatar.

Gwamnatin jihar Abia ta musanta korar ma'aikata 10,000
Gwamnatin Alex Otti ta ce ba ta kori ma'aikata 10,000 ba Hoto: Alex Otti
Asali: Twitter
"Rahoton cewa gwamna Alex Otti ya kori ma'aikata babu ƙamshin gaskiya a cikinsa." A cewarsa.

Kara karanta wannan

Yajin Aiki: Kungiyar Kwadago Reshen Jihar Kano Ta Sanar Da Sabbin Matakan Da Ɗauka

Ya bayyana cewa gwamnatin ta fito da wasu matakai domin magance matsalar ma'aikatan bogi, inda ya ƙara da cewa a dalilin hakan ne gwamnatin ta cire sunayen ma'aikatan bogi daga cikin albashinta, cewar rahoton Daily Post.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Menene dalilin korar wasu ma'aikatan?

"Wasu daga cikin ma'aikatan da sunayensu suka bayyana a wajen tantancewa ba a ɗauke su ta hanyar da ta dace ba, na daga cikin waɗanda abun ya shafa." A cewarsa.
"Wannan rukunin sun haɗa da waɗanda aka ɗauka aiki ba bisa ƙa'ida ba, a tsakanin watan Disamban 2022 har zuwa watannin Maris da Afirilu na wannan shekarar."

Kwamishinan ya bayyana cewa akwai hanyoyin da aka tsara wajen ɗaukar ma'aikata a jihar Abia.

Kanu ya bayyana cewa ba a bi ƙa'ida ba wajen ɗaukar su aiki sannan ya buƙaci al'ummar jihar Abia da su yi watsi da batun korar ma'aikata 10,000.

Kara karanta wannan

Hukumar DSS Ta Sako Dakataccen Karamar Hukumar Jihar APC da Ta Tsare, Bayanai Sun Fito

Gwamnan Jihar Gombe Ya Yi Karin Albashi

A wani labarin na daban kuma, kun ji cewa gwamnan jihar Gombe ya ƙarawa ma'aikatan jihar albashi, domin rage musu raɗaɗin da cire tallafin man fetue ya jawo a ƙasar nan.

Gwamna Inuwa Yahaya ya yi wa ma'aikatan ƙarin albashin N10,000 a kan kowane mataki a jihar, inda sabon tsarin albashin za a fara biyansa a watan Agusta.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng