Majaisa Ga Tinubu: Ka Yaye Takunkumin Daukar Ma'aikata a Najeriya

Majaisa Ga Tinubu: Ka Yaye Takunkumin Daukar Ma'aikata a Najeriya

  • Majalisa ta bukaci shugaba Tinubu ya cire takunkumin ɗaukar ma'aikata aiki a ma'aikatu da hukumomin gwamnatin tarayya
  • A cewar majalisar, shekaru da dama da suka shuɗe tsohon shugaban ƙasa ya kakaba takunkumin sakamakon matsin tattalin arzikin da aka shiga
  • Sai dai ta ce duba da halin da yan ƙasa ke ciki bayan cire tallafin fetur, ɗaukar matasa aiki zai sauƙaƙa wa talakawa

FCT Abuja - Majalisar wakilan tarayya ta buƙaci shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yaye takunkumin ɗaukar ma'aikata a ma'aikatu da hukumomin gwamnatin tarayya.

Rahoton The Nation ya tattaro cewa majalisar ta buƙaci shugaban ya cire takunkumin ne domin bada damar ɗaukar matasan 'yan Najeriya su cike guraben da ke akwai.

Zauren majalisar wakilan tarayya.
Majaisa Ga Tinubu: Ka Yaye Takunkumin Daukar Ma'aikata a Najeriya Hoto: Housengr
Asali: Facebook

Hakan ya biyo bayan muhawara da amince wa da kudirin da ɗan majalisar tarayya, Honorabul Francis Ejiroghene Waive, ya gabatar a zaman yau Laraba, 19 ga watan Yuli.

Kara karanta wannan

Da Dumi-Ɗumi: Gwamnan PDP Ya Kori Ma'aikata 1,700 Daga Aiki, Ya Umarci Su Dawo da Abinda Aka Ba Su

Majalisar ta kuma roki hukumar kula da ma'aikatan Najeriya da sauran hukumomin da abun ya shafa su hanzarta biyayya ga umarnin shugaban ƙasa kan wannan batu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Meyasa gwamnati ta kakaba takunkumin ɗaukar aiki a baya?

Honorabul Waive ya tuna lokacin da tsohuwar gwamnatin Buhari ta sanya takunkumin ɗaukar ma'aikata a ma'aikatu da hukumomin gwamnati sakamakon karyewar ɗanyen mai da faɗuwar tattalin arziki.

Haka zalika ya ƙara tuna lokacin da majalisar tarayya ta 9, wacce ta gabata ta cimma matsaya kuma ta buƙaci tsohon shugaban ƙasa ya cire takunkumin da ya ƙaƙaba.

Shin gwamnatin Buhari ta cire takunkumin a wancan lokacin?

A cewar ɗan majalisar, rahoton kafafen sada zumunta ya nuna cewa an cire takunkumin a wancan lokacin amma ba bu wata shaida ta ɗaukar ma'aikata a ko ina, Leadership ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Gwamna Ya Kori Baki Ɗaya Kwararrun Likitoci da Jami'an Lafiya a Jiharsa? Gaskiya Ta Bayyana

Ya ce tsawon shekaru ba a ɗauki sabbin ma'aikata ba, wanda hakan ya haddasa ƙarancin ma'aikata musamman a ɓangaren hukumomin tsaro, inda aka kara wa wasu girma, wasu kuma suka rasu.

Bugu da ƙari, ya ce cire takunkumin ɗaukar aiki da kuma ɗaukar matasa aiki zai zama wani ɓangare na yunkurin shugaban ƙasa domin rage wa mutane raɗaɗin cire tallafin mai.

Mambobin Kwamitin Gudanarwa Na APC Zasu Gana da Gwamnoni a Abuja

A wani rahoton na daban Mambobin kwamitin gudanarwa (NWC) na jam'iyyar APC ta ƙasa zasu sa labule da gwamnonin jam'iyyar yau Laraba.

NWC zata gana da gwamnonin ne a wani yunƙuri na neman goyon baya daga manyan masu ruwa da tsaki a jam'iyyar APC bayan murabus ɗin Abdullahi Adamu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262