Babbar Sallah: Hutun Sallah Da Sauran Ranakun Hutu 4 Da 'Yan Najeriya Za Su Yi Zuwa Karshen Shekarar 2023

Babbar Sallah: Hutun Sallah Da Sauran Ranakun Hutu 4 Da 'Yan Najeriya Za Su Yi Zuwa Karshen Shekarar 2023

A yanzu haka dai Musulman Najeriya dama sauran 'yan Najeriya baki ɗaya, na dakon Gwamnatin Tarayya ta sanar da ranakun hutun da ta ware domin shagulgulan bikin Sallah mai zuwa.

Ranakun da gwamnatin za ta bayar na nufin ba za a gudanar da ayyuka a ma'aikatun gwamnati, makarantu, bankuna, kasuwanni da sauransu ba a cikinsu.

Sultan ya ayyana Laraba a matsayin ranar babbar sallah ta bana
Sarkin Musulmi ya ayyana Laraba, 28 ga watan Yuni matsayin ranar babbar sallah. Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, Anas Azmah Assalafee
Asali: Facebook

Ana sa ran za a gudanar da bikin babbar sallah a Najeriya a ranar Laraba 28 ga watan Yuni. Ranar Larabar da kuma Alhamis 29 ga watan Yuni, za su kasance ranaku biyu na hutun babbar sallar ta bana.

Ranakun hutun da za a yi a Najeriya zuwa ƙarshen shekarar 2023

Legit.ng ta tattaro muku sauran ranakun hutun da ‘yan Najeriya za su yi daga nan har zuwa ƙarshen shekarar 2023, ga ranakun kamar haka:

Kara karanta wannan

NJC Ta Ba Da Shawarar Nada Ma'aikatan Shari’a 37 a Mukamai Daban-Daban, Jerin Sunaye

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

1. Laraba, 28 ga watan Yuni – Ranar farko ta hutun babbar sallah.

2. Alhamis, 29 ga watan Yuni – Rana ta ta hutun babbar salla.

3. Laraba, 27 ga Satumba – Hutun bikin Maulidi.

4. Lahadi, 1 ga watan Oktoba – Ranar tunawa da samun ‘yancin kai, Litinin, 2 ga watan Oktoba – Ranar hutun ‘yancin kai (saboda ranar tunawa da ’yancin kai ta faɗo a ranar Lahadi).

5. Litinin, 25 ga watan Disamba - Ranar Kirisimeti.

6. Talata, 26 watan Disamba – Ranar Dambe ta duniya.

Yadda Gwamnatin Tarayyar Najeriya ke sanar da ranakun hutu ga 'yan ƙasa

Ma'aikatar harkokin cikin gida ce aka ɗorawa alhakin sanar da ranakun hutu ga 'yan Najeriya, in ji wani rahoto da BBC Pidgin ta wallafa.

Ma'aikatar na sanar da ranakun da Gwamnatin Tarayya ta ware a matsayin ranakun hutu ga 'yan ƙasar baki ɗaya.

Kara karanta wannan

Matsalar Tsaro: Gwamna Lawal Ya Fara Ɗaukar Matakan Kawo Karshen Yan Bindiga a Zamfara

Hakanan, duk wata ranar hutun da ta faɗo a cikin kwanakin ƙarshen mako, za a ayyana ranar mako ta gaba a matsayin ranar hutun.

Dalili kuwa shi ne domin a mayar da ranar hutun a cikin kwanakin aiki, saboda mutane sun riga da sun saba da hutawa a ranakun ƙarshen mako.

Sarkin Musulmi ya sanar da ranar Idin babbar sallah

A baya Legit.ng ta rahoto cewa mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III, ya ayyana ranar Laraba 28 ga watan Yuni a matsayin ranar Idin babbar sallah na shekarar 1444 AH/2023.

Sarkin Musulmi, wanda shine shugaban majalisar ƙoli ta addinin Musulunci ta Najeriya, ta hannun fadar sarkin da ke Sokoto, ya bayyana hakan a daren Lahadi, 18 ga watan Yuni, a wani sako da Legit.ng ta tsinkayo a shafin kwamitin ganin wata na Tuwita.

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Litinin a matsayin ranar hutun dimokuraɗiyya

Kara karanta wannan

Babbar Kotu Ta Sauya Hukunci Kan Batun Tsige Shugaban Yan Sanda Na Ƙasa IGP Usman Baba

A kwanakin baya 'yan Najeriya sun mori ranar hutun dimokuraɗiyya da Gwamnatin Tarayya ta bayar a ranar Litinin, 12 ga watan Yunin shekarar 2023 da muke ciki.

Ana dai yin bikin ita wannan rana ta dimokuraɗiyya ne domin tunawa da irin gwagwarmayar da 'yan baya suka sha wajen ganin cewa dimokuraɗiyya ta kafu da ƙafafuwanta a Najeriya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Deen Dabai avatar

Deen Dabai Zaharaddeen Hamisu marubuci kuma ma'aikacin jarida ne da ke da gogewa wajen iya tantance sahihan labarai da na karya. Ya yi digirinsa a jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Baya ga haka, ya shafe sama da shekaru 5 a bangaren aikin watsa labarai wanda hakan ya bashi gogewa ta musamman a aikin jarida. Za a iya tuntubarsa ta adireshinsa na yanar gizo: deen.dabai@corp.legit.ng

Online view pixel