Abubuwa 6 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Tsohon Daraktan Ayyuka Na EFCC, Mohammed Abba

Abubuwa 6 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Tsohon Daraktan Ayyuka Na EFCC, Mohammed Abba

Mohammed Umar Abba, ya kasance tsohon daraktan ayyuka na hukumar yaki da cin hanci da hana yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC).

A ranar Laraba, 14 ga watan Yuni ne sunan Umar Abba ya sake bayyana a kanen labarai bayan an kuskure shi a matsayin wanda zai zama mukaddashin shugaban hukumar EFCC bayan dakatar da Abdulrasheed Bawa, shugaban EFCC da Shugaban kasa Bola Tinubu ya yi.

Sai dai kuma, an gano ba shine zai gaji Bawa ba domin dai ba shine daraktan ayyuka na hukumar mai ci ba kamar yadda aka dunga yayatawa.

Mohammed Abba
Abubuwa 6 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Mukaddashin Shugaban EFCC, Mohammed Abba Hoto: Punch
Asali: UGC

Abba ya taba rike mukamin mukaddashin shugaban hukumar ta EFCC a lokacin da aka dakatar da tsohon mukaddashin shugaban hukumar, Ibrahim Magu a 2020.

Ga wasu abubuwa shida ya ya kamata ku sani game da tsohon daraktan ayyuka na hukumar EFCC:

Kara karanta wannan

Jerin Manyan Jami’an Gwamnati 1 Da Shugaban Kasa Tinubu Ya Dakatar Cikin Makonni 2

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

1. An haifi Mohammed Umar Abba a ranar 22 ga watan Yunin 1965 a karamar hukumar Tudunwada ta jihar Kano.

2. Abba ya yi digirinsa na farko a jami'ar Bayero, Kano. ya yi bautar kasarsa a hukumar yan sandan tsohuwar jihar Anambra sannan daga bisani ya samu shiga rundunar yan sandan Najeriya. Ya halarci makarantar yan sanda ta Kaduna, jihar Kaduna.

3. CP Abba ya samu amincewar hukumar a watan Janairun 2016 domin ya jagoranci sashin bincike na CTG1, wani bangare a hedkwata da ke Abuja.

4. An nada shi daraktan ayyuka na hukumar a 2017.

5. A 2019, an kara masa girma zuwa mukamin kwamishinan yan sanda.

6. A ranar 9 ga watan Yulin 2020, Abba ya zama mukaddashin shugaban hukumar, kasancewarsa jami'i mafi girma a sashin ayyuka lokacin da aka dakatar da tsohon shugaban EFCC, Ibrahim Magu.

Kara karanta wannan

Tsohon Sanatan PDP Ya Zama Babban Mai Yabon Gwamnatin Tinubu Dare da Rana

Shugaban kasa Bola Tinubu ya dakatar da Abdulrasheed Bawa daga matsayin shugaban EFCC

A gefe guda, mun kawo a baya cewa shugaban kasa Bola Tinubu ya dakatar da Abdulrasheed Bawa, shugaban hukumar yaki da cin hanci da hana yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC) har sai baba-ta-gani.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Willie Bassey, daraktan labarai na ofishin sakataren gwamnatin tarayya ya saki a ranar Laraba, 14 ga watan Yuni.

Bassey ya ce dakatarwar da aka yi wa Bawa ya biyo bayan manyan zarge-zarge da ake yi masa na cin mutuncin kujerarsa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng