English, 98; Biology, 94: Daliba ’Yar Shekara 16 Ce Ta Fi Kowa Cin Jarrabawar JAMB

English, 98; Biology, 94: Daliba ’Yar Shekara 16 Ce Ta Fi Kowa Cin Jarrabawar JAMB

  • Ejikeme Joy, wata daliba a makarantar sakandare ta mata ta Anglican a karamar hukumar Nnewi a jihar Anambra ta fi kowa cin jarrabawar UTME a bana
  • Joy ta samu maki mai daukar hankali a dukkan darussa hudu da ta rubuta, inda ya samu jumillar maki 362 a UTME
  • Kwamishinan ilimi a jihar Anambra, Farfesa Ngozi Chuma-Udeh, ta yi martani game da kwazon wannan daliba

Nnewi, jihar Anambra Wata daliba a makarantar sakandaren mata ta Anglican da ke Nnewi a jihar Anambra, Ejimeke Joy ya dauki hankalin jama’a bayan lashe maki mai tsoka jarrabawar UTME.

Rahoton da Legit.ng Hausa ke samu ya bayyana cewa, dalibar ta samu maki 362 a jarrabawar da hukumar JAMB ke shirya a duk shekara.

Wakilinmu a jihar Anambra, Mokwugwo Solomon ya gano adadin makin da dalibai ta samu kan kowane darasi da ta rubuta a jarrabawar.

Kara karanta wannan

Sanatocin Arewa 2 Sun Janye Daga Takarar Shugaban Majalisar Dattawa, Sun Koma Bayan Wani

Dalibar da ta ci JAMB din da ya fi na kowa
Yadda daliba ta ci JAMB fiye da kowa a Najeriya | Hoto: Mokwugwo Solomon
Asali: UGC

Makin da Joy ta samu

  1. English - 98
  2. Physics - 89
  3. Biology - 94
  4. Chemistry – 81

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Gwamnatin Anambra ta yi martani

Wata sanarwar da sakataren yada labarai ga gwamna Charles Soludo. Christian Aburime a ranar Asabar ta yaba da kokarin da dalibai ta yi wajen nuna kwazo a jarrabawar.

Hakazalika, sanarwatr ta bayyana alfahari da dalibai da kuma bayyana irin tasirin da gwamna Soludo ke yi wajen ciyar da ilimi gaba a jihar da ke Kudancin Najeriya.

Idan baku manta ba, hukuamar jarrabawa ta JAMB ta saki sakamakon jarrabawar daliban da suka rubuta UTME na shiga makarantun gaba da sakandare a bana.

Hakan ya dauki hankali matuka, inda daliban da yawa ke bayyana adadin makin da suka samu a wannan shekarar.

Yadda ake duba sakamakon UTME na 2023

Kara karanta wannan

Ekweremadu: Abu 5 Game Da Tsohon Mataimakin Majalisar Dattawar Najeriya Da Aka Yanke Wa Shekara 10 a Birtaniya

A wani labarin, mun kawo muku yadda ake duba sakamakon jarrabawar UTME ta 2023 da aka rubuta a wannan shekarar cikin watan Afrilun da ya gabata.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwar da hukumar ta fitar, inda ta bayyana yadda ake duba sakamakon da kuma wadanda ba za su samu damar ganin sakamakon jarrabawar ba saboda wasu dalilai.

A cewar JAMB, duk dalibin da ke son duba sakamakonsa, to zai tura sakon tes ne da layin da ya yi rajistar UTME a bana (UTMERESULT zuwa lamba 55019 ko 66019).

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.